Rundunan Yan sanda a jahar Adamawa ta lashi takwabin hukunta duk Wanda aka samu dayiwa doka Karan tsaye a lokacin bikin samun yanci.
Rundunan yan sandan jahar Adamawa tare da takwarorinta zasu daukai dukkanin mataki da suka dace domin dakile dukkanin masu yin amfani da bikin ranan yanci wajen zanga zanga saboda haka a shirye suke su shiga kafar wando Daya da duk wadanda keyiwa zaman lafiya Jahar barazana.
Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.
Sanarwan tace rundunan ta tunin da sanya ido tare da tura Jami anta wuwaren taruwar jama a domin ganin ko a kwai Wanda zai karya doka.
Sanarwan ta kirayi Al umma da sukasance masu taimakawa hukumomin tsaro da wasu bayanain da zai taimaka wajen takawa masu yiwa zaman lafiya barazana birki.
Comments
Post a Comment