KUNGIYAR MAFARAUTA A NÀJERIYA DAKE YANKIN AREWA MASAU GABAS TA LASHI TAKWABIN MARAWA HUKUMOMIN TSARO BAYA DOMIN SAMAR DA ZAMAN LAFIYA MAI DAUREWA.
Daga Alhassan Haladu Yola. Kungiyar mafarauta dake yankin arewa masau gabas ta tabbatar da aniyarsa na taimakawa hukumomin tsaro domin ganin an Samu zaman lafiya mai daurewa a yankin dama kasa baki Daya. Shugaban kungiyar Mafarauta na yankin arewa masau gabas Modibbo Idris Usman Tola ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai a Yola. Modibbo Idris Usman Tola ya ce su aikin sune taimakawa hukumomin tsaro domin ganin an Samu damar dakile matsalar tsaro, domin ganin manoma da makiyaya sun gudanar da harkokinsu cikin kwanciuar hankali. Modibbo Usman Tola yace kawo yanzu an Samu cigaba sosai wajen Samar da tsaro, saboda haka akwai bukatar Samun hadin Kai a tsakanin hukumomin tsaro da Al umma domin a cewarsa hakan ne zai taimaka wajen Samar da zaman lafiya mai daurewa. Ya Kuma kirayi Al umma da su Kara himma wajen taimakawa Jami an tsaro da wasu bayanai da zasu taimaka wajen dakile aikata laifi, domin Samar da cigaba. Ya Kuma shawarci jama a da su Daina daukan doka a hanu, sukasa...