Dan Takararmu Na Gwamna ba Makaryaci ba ne....Dr Ahmed Gana
By Abdullahi Tukur Dr. Jamil Isyaku Gwamna, Sardaunan Gombe, ba sabon suna ba ne a fagen siyasar Jihar Gombe. A duk inda kaji an kira sunansa, babu abinda yake biyo baya face, Nagarta, Aminci, Yabo, Jinjina da Sambarka. Dr Ahmed Gana, tsohon kwamishinan lafiya na Jihar Gombe ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a Gombe. Sardauna ya kasance Dan Jihar Gombe daya fito daga gidan manya wanda hakan ya bashi damar samun kyakkyawar tarbiyya da Ilimi mai nagarta. Jamil Gwamna Mutum ne mai hidima ga al'umma ga kyauta ga kuma son jamaa, kamar yadda mahaifinsa yake. Sardaunan Gombe Mutum ne mai kishin jiharsa, mai son ci gabanta, kuma wanda ya shafe shekaru sama da 20 yana gina kyakkyawar alaka da al’ummar jihar tare da bayar da gudummawa wajen inganta rayuwar matasa da sauran jama’a. Sardauna mutum ne mai ilimi da kwarewa. Dokta ne a fannin tattalin arziki, kuma gogaggen ma’aikaci da ya yi aiki a hukumomin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu. Wannan kwarewa ta ba shi...