Gwamnatin tarayya ta Horan da Yaran Matan Chibok sana o I daban daban a jahar Asamawa.
Daga Alhassan Haladu Yola. Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ma aikatar harkokin mata a Najeriya ta koyawa yaran matan chibok Wanda aka cetosu daga hanun masu garkuwa da mutane sana o I daban daban domin dagaro da kansu. Yaran mata akalla 18 ne dai suka Samu horon wadanda suka koyi sana o I da suka hada da dinki, da dai sauransu Wanda hakan zai taimaka wajen inganta rayuwarsu yadda ya Kamata. Bikin yaye yaran matan dai ya gudana ne a Jami ar Modibbo Adama dake Yola a jahar Asamawa. Da take jawabi ministar harkokin mata a Najeriya Hajiya Imaam Ibrahim Suleiman tace gwamnatin tarayya ta dauki matakin haka ne duba da yadda yaran mata suka tsinci kansu a ciki Wanda haka ya sasu cikin damuwa, saboda haka ya Kamata a koya musu sana o I da zasu dogara da kansu domin inganta rayuwarsu. Ministan ta Taya wadanda aka yaye murna tare da Kiran su da sukasance masu amfani da abinda aka koya musu ya hanyar da ta dace domin bunkasa harkokinsu domin su zama abin koyi ga na gaba. Imaam Ibrahim ...