A yayinda aka fuskanci Babban zaɓen shekara ta 2027 an kirayi matasa da mata da su tabbata sun mallaki katin zabe.
Daga Alhassan Haladu Yola. Domin an dama da su a harkokin Siyasa an kirayi matasa da mata da su tabbata sunje suyi rijistan katin zabe, ga wadanda sukayi rijista kuwa su tabbatar sun karbi katin zabe su Wanda hakan ne zai basu damar zaban shuwagabanin da suke so a lokacin Babban zaɓen shekara ta 2027. Mrs Comford Ibrahim Wanda itace Ko odinatan mata a siyasa wato women in politics dake Yan kin arewa masau gabasa ita tayi wannan Kira a zantawarta da manema labarai a Yola. Mrs Comford Ibrahim tace mata da matasa sune suke da Kaso Mafi tsoka a kada kuri a don haka ta jaddada kiranta ga mata da matasa da kada suyi kasa a gwiwa wajen yin rijistan katin zabe domin da katin ne za su zabi Wanda zai cire musu kitse a wuta. Mrs Comford ta Kuma shawarci mata da matasan da kada wasu su rudesu ranan zabe da abinda ba zai magance musu matsalar suba su tabbata sun zabi shugaban da zai kare musu martanarsu dama sama musu aikinyi. A cewar Mrs Comford dai mata da matasa sun gaji da gafara sa ba su...