Ma aikatar ilimi a jahar Adamawa ta rarranawa manyan makarantu sakandare dake fadin jahar.
Daga Alhassan Haladu Yola. Gwamnatin jahar Adamawa ta ma aikatar ilimi ta rarranawa daukacin manyan makarantu sakandare dake fadin jahar Adamawa takardun karatu a Wani mataki na bunkasa ilimi a fadin jahar Adamawa. An dai rarraba takardun ne a makarantar kwalejin tunawa da General Murtala Muhammed dake Yola a jahar Adamawa. Da yake jawabi a yayin kaddamar da rarraba takardun kwamishinan ilimi dake jahar Adamawa Dr Garba Pella yace wannan rarraba takardun Yana daga cikin aniyar gwamnati in inganta tare da bunkasa ilimi a tsakanin dalube dake fadin jahar Adamawa. Dr Garba Pella yaja hankalin shuwagabanin makarantu da su Maida hankali sosai wajen kula da kayakin da aka basu Wanda hakan zai taimaka wajen baiwa Yara ilimi da ya Kamata. Ya Kuma sake jaddada aninyar gwamnatin nayin dukkanin abinda suka dace domin ganin dukkanin dalube sunyi sanaran cin jarabawar kammaka sakandare da sakamoko mai kyau don haka gwamnati ta kimtsa tsaf domin ganin an baiwa Yara ilimi kyau...