MASU RUWA DA TSAKI DAKE CIKIN JIMETA SUN BUKACI ABBATI YA TSAYA DANTAKARAN SANATA.
Daga Alhassan Haladu Yola. Al umma cikin garin Jimeta dama masu ruwa da tsaki sun bukaci da Aliyu AbdulHamid Wanda akafi Sani da Abbati da ya fito ya tsaya takaran Dan majalisar dattawa Wanda zai wakilci mazabar Adamawa ta tsaki a majalisar dattatwar Najeriya, a zaษen shekara ta 2027. Hakan na zuwane a Babban taro da Al ummar Jimeta suka gudanar Wanda ya Samu halartan dukkanin masu ruwa da tsaki dake cikin garin Jimeta. Hon. Suleiman P A memba mai wakiltar karamar Hukumar Yola ta arewa a majalisar dokokin jahar Adamawa, ya baiyana farin cikinsa dangane da wannan taro musammanma kan bukatan Abbati ya tsaya takaran Santa, Wanda hakan abin farin ckine, saboda ya taka rawan gani a lokacin da yake rike da NISAL. don haka a shirye suke su mara masa baya domin ganin ya cimma nasara domin ceto Al ummar Jimeta. Da yake gabatar da nashi jawabi Alhaji Isa Bagalci ya jaddada cewa Abbati ya gudanar da aiyukan cigaba a fannoni daban daban saboda haka ya zama wajibi su mara masa baya domin ya c...