An bukaci mata musulmai da suyi rijista katin zabe da Kuma shiga kwamitin women in Da awa dake jahar Adamawa.
Daga Alhassan Haladu Yola. An kirayi daukacon mata musulmai da su zo su shiga kwamitin women in Da awa domin gudanar da aiyukan cigaban addinin musulunci yadda ya Kamata. Ko odinatan Kwamitin women in Da aw a jahar Adamawa Hajiya Rabi atu Ahmed Buhari ce tayi wannan Kira a zantawarta da manema labarai a Yola. Hajiya Rabi atu Ahmed Buhari ta baiyana cewa akwai bukatar mata sukasance masu Bada gudumawa wajen Gina Addinin musulunci a Koda yaushe, saboda haka tana Kira da Babbar murya ga mata musulmai da su shugo cikin kwamitin women in Da awa domin Bada tasu gudumawa wajen cigaban addinin musulunci. Hajiya Rabi atu Ahmed tace akwai aiyuka da dama Wanda ya Kamata ace mata musulmai sun Bada hadin Kai da goyon baya, Wanda hakan zai taimaka wajen cigaban addinin musulunci yadda ya Kamata. Hajiya Rabi atu tace kawo yanzu suna gudanar da taro a kowace ranan lahadi na karshen wata a makarantar GRA dake daf da karantar FOMWAN, Saboda haka akwai bukatar mata suzo su shiga da Kuma karban Form...