MAJALISAR ADDININ MUSULUNCIN JAHAR ADAMAWA TA YANTA MUTUM SHIDA DAGA GIDAJEN YARI A JAHAR ADAMAWA.
Daga Alhassan Haladu Yola. Majalisar Addinin Musulunci a jahar Adamawa ta yanta mazauna gidan yari shida tare da taimakawa da kayakin abinci was gidajen yarin uku dake cikin kananan hukumomi Yola ta arewa Yola ta kudu dake jahar Adamawa. Majalisar ta yanta mazauna gidan yarin ne a zyara da ta Kai a gidajen yarin Jimeta dake karamar Hukumar Yola ta arewa, sai na Youlde Pate, da na Yola wadanda ke karamar Hukumar Yola ta kudu a jahar Adamawa. Da yake yiwa mazauna gidan yarin jawabi shugaban majalisar Addinin musulunci Kuma shine ya jagoranci tawagan majalisar domin Kai ziyaran Mallam Gambo Jika yace sun kasance a gidajen yarin ne duba da yadda ake cikin kwanaki goma na karshen Ramadan Wanda a lokacin ne ake rubaiyya ibadu da Kuma aikata Alheri. Saboda haka ne ma suka ga ya dace su kawo ziyara gidajen yarin tare da taimakawa da kayakin abinci, dama yanta wasu da cikin mazauna gidajen yarin. Mallam Gambo ya Kuma shawarci mazauna gidajen yarin da sukasance masu canja halayensu da Kuma...