An bukaci Al umma sukasance sun mallaki katin zabe domin zaban shuwagabanin da sukeso
Daga Alhassan Haladu Yola. Domin ganin an gudanar da Zabe cikin tsanaki da kwanciyar hankali an kirayi Al umma da sukasance sun mallaki katin zabe su Wanda hakan ne zai basu damar zaban shuwagabanin dake suke so a Babban zaษen shekara ta 2927. Mataimaki na musamman ga gwamna Ahmadu Finti kan harkokin jama a Barista Sunday Wugira ne ya Yi wannan Kira a zantawarsa da manema labarai a Yola. Barista Sunday Wugira yace Yana da muhimmanci Al umma musammanma wadanda suka cancanci mallakar katin zabe da su gaggauta mallakar katin zabe domin shine zai basu damar zaban shugaban da zai cire masa kitse a wuta. Wugira ya baiyana cewa an Dade ana gudanar da mulkin siyasa Amma cigaba da aka Samu Bai taka Kara ya karyaba, saboda haka Yana da muhimmanci Al umma suyi karatun ta nitsu wajen zaษen shugaban da ya cancanci ya kagorancesu. Barista ya shawarci masu zabe da kada su bari a rudesu ko a yaudaresu Kamata yayi su Maida hankali da taka tsan tsan wajen zakulo shuwagabanin da zasu shugaban...