TSARO: AN BUKACI YAN NAJERIYA SUKASANCE MASU BAIWA HUKUMOMIN TSARO HADIN KAI DA GOYON BAYA.
DAGA Alhassan Haladu Yola. A yayinda Najeriya ke fuskantar kalubalen tsaro an kirayi Yan Najeriya da sukasance suna baiwa hukumomin tsaro hadin Kai da goyon baya domin ganin sun cimma burinsu na inganta tsaro a fadin Najeriya baki Daya. Kwammanda Mafarauta na kasa Kuma sarkin yakin mafarautar Adamawa Alhaji Muhammed Adamu ne yayi wannan Kira a zantawarsa da manema labarai a Yola, fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Muhammed Adamu yace baiwa hukumomin tsaro hadin Kai Yana da mutukan muhimmanci Wanda acewarsa hakan zai Karawa hukumomin tsaron kwarin gwiwa wajen gudanar da aiyukansu na tsaron kasa. Muhammed Adamu yace ya Kamata Al ummar Najeriya sukasance suna taimakawa hukumomin tsaro irinsu, rundunan sojoji, Yan sandan, civil defence, Mafarauta da dai sauransu, da wasu bayanai da zai taimaka wajen dakile aikata laifuka a fadin Najeriya. Ya Kara da cewa ta baiwa hukumomin tsaron goyon bayane za a Samu damar kawar da Bata gari a jahar tsakanin Al umma baki Daya. Saboda haka Yana da muhi...