Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta ceto yaran mata biyu wadanda akayi yunkurin safaransu zuwa kasar Ghana.
Daga Alhassan Haladu Yola. Rundunan Yan sandan jahar Adamawa tayi nasaran kama Wanda ake zargi da safaran mutane.tare da ceto mata biyu wadanda akayi aniyar safaransu. A kokarinta na yaki da safaran mutane dama aikata laifuka rundunan Yan sandan jahar Adamawa tayi nasaran dakile aiyukan safaran mutane. Kayakin rundunan Yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje me ya Samar da haka a wata sanarwa da yaranawa manema labarai a Yola. A ranan 12 -11-2025 rundunan ta sashin tattara bayanai sirri dake Nan Yola. Biyo bayan bayanai sirri da ta Samu Wanda hakan yakaita da Samun nasaran tsare Wani mai suna Hamza Hammantukur Isa mai shekaru 40 da haifuwa Kuma mazaunin a titin Bauchi dake cikin karamar Hukumar Yola ta Arewa, Wanda ake zargi ya kware wajen yin safaran yaran mata daga Adamawa zuwa Ghana domin sasu yin karuwanci, Kuma Yana yaudaransune ta Samar musu da aiki, da zasu Samu kudi mai yawa. A lokaci aka gudanar da sintiri dangane da lamaein an ceto yaran mata biyu masu ...