AN KIRAYI GWAMNATIN TARAYYA DANA JIHOHI DA SU SAMARWA MANOMA ALBASA WURAREN ADANA ALBASA A FADIN NAJERIYA.
Daga Alhassan Haladu Yola. Wani mataki na bunkasa harkokin Albasa a fadin Najeriya an kirayi gwamnatin tarayya da na jihohi dama masu ruwa da tsaki da suyi dukkanin abinda suka dace domin samarwa manoma Albasa wuraren adana Albasa domin basu damar bunkasa harkokin su yadda ya Kamata a fadin Najeriya. Shugaban kungiyar Manoma Albasa A Najeriya Aliyu Isa Maitasamu ne ya baiyana haka a zantawarsa da Jaridar An Nur hausa. Aliyu Isa yace abinda yake ciwa manoma Albasa tuwo a kwarya shine rashin wuraren adana Albasa Wanda hakan Yana haifar musu da koma baya a harkokin su na noman Albasa, saboda haka akwai bukatan gwamnatocin jihohi da na tarayya da su taimaka su shiga tsakani domin inganta noma Albasa. Aliyu Isa yace Najeriya itace na Daya a noma Albasa saboda daukacin jihohin Arewacin Najeriya suna noma Albasa, Kamata yayi a Maida hankali wajen noma Albasa, domin noman Albasa Yana farfado da tattalin Arziki a kasa. Aliyu ya tabbatar da cewa kungiyarsu a shirye take wajen y...