An bukaci malamai da su fadada aiyukansu wajen wayarwa matasa kai

An kirayi malamai da su kara fadada wa azuzzukasu zuwa lunguna da sako sako dake fadin jahar Adamawa dama fadakar da matasa dangane da muhimmancin neman ilimin addini dama samar da zaman lafiya a tsakanin al ummah. Hakimin Gombi Alhaji Usman Ibrahim sarkin fada ne yayi wannan kira a lokacinda majalisar addinin musulunci a jahar Adamawa ta shirya taron Da awa a karamar hukumar ta Gombi. Hakimin yace matasa su suke da kaso masu yawa a tsakanin al ummah don haka ya kamata a maida hankali akansu ta wajen nuna masu muhimmancin hadin kai da kuma neman ilimi wanda acewarsa hakan zaitaimaka wajen samar da zaman lafiya maidaurewa. Don haka ya kamata malamai su dukufa wajen Jan hankalin matasan a koda yaushe tare da shawartan iyaye da kuma su hada tasu gudumawar wajen fadakar da matasa dangane da yadda zasu inganta rayuwarsu yadda ta kamata. Ya kuma kirayi masu rike da masarautun gargajiya da suma sukasance masu bada hadin kai wajen wayarwa matasan kai domin ganin an samu nasaran wayarwa matasan kai yadda ya kamata.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie