An bukaci wadanda sukayi rijistan katin zabe da suje su karbaibi katin zabensu domin su samu damar kada kuri a.

An kirayi al umma musammanma wadanda sukayi rijistan katin zabe ta suje su karbi katinsu wanda hakan ne zai basu damar jefa kuri a a ranan zaben shekara da dubu biyu da ashirin da uku. Jami I mai hulda da jama a na hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa shiyar jahar Adamawa Dahiru Jauro ne ya yi wanan kira a lokacin da yake jawabi a wurin taron kungiyar limamai na jahar Adamawa wanda ta shirya a yola. Dahiru Jauro yace akwai mutane da dama wadanda sukayi rijista amman har yanzu basu je sun karbi katunsuba wanda kuma hakan koma bayane musammanma ga su wadanda sukayi rijistan katin zaben. Ya kuma kirayi limamai da suma su bada tasu gudumawar wajen fadakar da al umma dangane da muhimmancin katin zaben domin mallakan katin zaben shine yancinsu. Shima a jawabins malam Muhammadu Umar Zingina kiran limamain yayi da su kasance masu koyi da halayen Annabi Muhammadu (S A W) ta yadda ya gudanar da shugabancinsa ga al ummah. Malam Salihu Dauda Babban limamin Masallacin Jumma a na bayan kasuwa ya baiyana jin dadin dangane da taron da aka shirya domin wayar musu da kai dangane da yadda zasu gabatar da fadakar da al umma dangane da zaman lafiya da kuma ganin an kammala Babban zaben shekara ta 2023 cikin kwanciyar hankali ba tare da matsalaba.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.