An bukaci Babban Bankin Najeriya ya wadatar da sabbin kudade.

Masu sana ar fawa a jahar Adamawa sun koka dangane da karancin kudi da ake fuskanta biyo bayan canja fasalin kudin Najeriya wanda haka yayi sanadiyar koma bayan harkokin kasuwancinsu na fawa. Alhaji Babanna Palace ne yayi wannan kira a tattaunawarsa da jardar Al Nur a yola. Dangane da karancin kudi da ake samu. Babanna yace ya kamata gwamnatin ta duba yanayinda al umma ke ciki na matsalar rayuwa domin ta dauki matakin magance matsalar. Wanda acewarsa mutane sun shiga wani yanayi na matsin rayuwa. Babanna yace Babban matsalarma itace wasu masu shanun basu da asusun ajiya a banki bale a tura musu kudi don haka ne ya zama wajibi su kirayi gwamnati da ta dubi lamarin domin samawa al umma saukin rayuwa. Da wannan ne yake kira ga Babban Bankin Najeriya da ya wadata bankuna da sabbin kudaden domin ganin al umma sun samu saukin gudanar da harkokinsu yadda ya kamata ba tare da matsalaba. Ya kuma kirayi yan Najeriya da sukasance masu gudanar da adu o i a koda yaushe domin neman taimakon Allah Madaukakin sarki wajen kawo karshen dukkanin kalubalen rayuwa da al umma ke fuskanta. Ya kuma yi adu ar gani an kammala zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku lafiya .

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie