An samu gawar wani yaro da aka cire sassan jikinsa.

A safiyar lahdin nan ne aka wayi gari da ganin gawar wani yaro karami mai kimani shekaru sha biyu, wanda aka cirewa maqoshi da idanu da kuma harshe, sannan aka jefar dashi a wani lungu a unguwar Rumde dake bayan sakatariyar karamar hukumar Yola ta Arewa a Jihar Adamawa. Ana kyauta ta zaton Yaron Almajiri ne da har zuwa lokacin hada wannan Rahoton ba'a kai ga gano a wace makaranta yake karatu ba. Sai dai duk kokarin da akayi domin jin ta bakin mazauna unguwar da lamarin ya faru, Mutanen duk sunki cewa uffan kan lamarin Wani jami'in tsaro daga Jimeta Division ya tabbatar da cewa sun dauki gawar zuwa mutuware dake asibitin kwararru na specialist dake jimeta.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.