An samu gawar wani yaro da aka cire sassan jikinsa.

A safiyar lahdin nan ne aka wayi gari da ganin gawar wani yaro karami mai kimani shekaru sha biyu, wanda aka cirewa maqoshi da idanu da kuma harshe, sannan aka jefar dashi a wani lungu a unguwar Rumde dake bayan sakatariyar karamar hukumar Yola ta Arewa a Jihar Adamawa. Ana kyauta ta zaton Yaron Almajiri ne da har zuwa lokacin hada wannan Rahoton ba'a kai ga gano a wace makaranta yake karatu ba. Sai dai duk kokarin da akayi domin jin ta bakin mazauna unguwar da lamarin ya faru, Mutanen duk sunki cewa uffan kan lamarin Wani jami'in tsaro daga Jimeta Division ya tabbatar da cewa sun dauki gawar zuwa mutuware dake asibitin kwararru na specialist dake jimeta.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie