Posts

Showing posts from June, 2023

An kirayi gwamnatocin jihohi dana kananan hukumomi da su maida hankali wajen tallafawa manoma . Manu Ngurore.

Image
An kirayi gwamnatin jihohi dana kananan hukumomi da su maida hankali wajen taimakawa manoma a koda yaushe domin samun cigaban harkokin noma dama bunkasa tattalin arziki baki daya. Alhaji Usman Abubakar wanda kuma shine sakataren kungiyar manoma auduga a jahar Adamawa ne yabaiyana haka azatawarsa da manema labara a yola. Alhaji Usman yace kawoyanzu gwamnatin tarayyace kawai da ke taimakawa manoma wanda kuma hakan yasa manoman ke fuskatar kalu bale da dama, don haka akwai bukatar gwamnatin jihohi dana kananan hukumomi suma sukasance suna tallafawa manoman domin ganin an samu wadaceccen abinci a fadin Najeriya baki daya. Alhaji Abubakar ya kara kira da cewa gwamnatocin sukasance suna taimakawa manoman da kayakin noman akan lokaci wanda hakan zai baiwa manoman damar gudanar da aiyukansu yadda ya kamata. Ya kuma shawarci gwamnatocin da su maida hankali wajen shiryawa manoma taron bita musammanma wadanda ke yankunan karkara domin fadakar dasu yadda ake guadanar da harkokin noma

Rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta dauki dukkanin matakai domin bada kariya alokacin bukukuwarBabban Sallah.

Image
Runduna yan sandan jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin bada kariya ga al umma musulmai domin ganin an gudanar fa bukukuwar Babban Sallah lafiya ba tare da matsalaba. Kakakin runduna yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ba baiyana haka a yayinda ake daf dafara bukukwar Babban sallah na wannan shekara. Sanawar dai nacewa anjiyo kwamishinan yan sandan jahar ta Adamawa Afolabi Babatola nacewa rundunan ta dauki dukkanin matakai da ya kamata domin bada kariya a wurare bukukuwar dake sasssa daban daban a fadin jahar. Don haka nema kwamishinan ya umurci mataimakinsa mai kula da sashin aiyuka da yayi dukkanin abinda suka dace domin tabbatar da cewa komai ya gudana cikin kwanciuar hankali musammanma a wuraren da za a gudanar da sallar idi a fadin jahar ta Adamawa baki daya. Har wayau rundunan tasha alwashin saka kafar wando daya ga duk wanda kekokarin karya doka ko kuma yiwa doka Karen tsaye domin rundunan baza ta lamicewa duk wanda ya karya dokaba. Da wan

Kungiyar Sullunawa a jahar Adamawa ta kudiri aniyar kawo kashen rikici a tsakanin manoma da makiyaya.

Image
A yayinda damina ke karatowa ne da an kirayi manoma da makiyaya da sukasance masu fahintar juna da hada kansu a koda yaushe domin samun zaman lafiya a tsakaninsu da ma cigaban aiyukansu yadda ya kamata ba tare da matsalaba. Shugaba kungiyar Sullubawa ta kasa NASAN shiyar jahar Adamawa Alhaji Bello Ardo ne yayi wannan kira a lokacinda yake zantawa da manema labarai a Yola. Alhaji Bello Ardo yace ya zama wajibi suja hankalin manoma da makiyaya duba da yadda aka fuskaci damina wanda kuma alokaci daminane akafi samun rikici a tsakanin manoma da makiyaya. Don hakane ya kamata akirayi manoma da makiyayan da sukasance masu kai zuciya nesa a duk lokacinda wani abu ya shiga tsakaninsu. Alhaji Bello yace manoma da makiyaya su sanifa su yan uwan junane don haka bai kamata ace ana samu ta kaddama a tsakaninsuba. Saboda haka ya kamata sukasance masu doka da ka ididin noma da kiwo a koda yaushe. Bello ya kuma kara da cewa sun tattauna da kwamandan rundunan tsaro farin kaya wato civil