Kungiyar Sullunawa a jahar Adamawa ta kudiri aniyar kawo kashen rikici a tsakanin manoma da makiyaya.

A yayinda damina ke karatowa ne da an kirayi manoma da makiyaya da sukasance masu fahintar juna da hada kansu a koda yaushe domin samun zaman lafiya a tsakaninsu da ma cigaban aiyukansu yadda ya kamata ba tare da matsalaba. Shugaba kungiyar Sullubawa ta kasa NASAN shiyar jahar Adamawa Alhaji Bello Ardo ne yayi wannan kira a lokacinda yake zantawa da manema labarai a Yola. Alhaji Bello Ardo yace ya zama wajibi suja hankalin manoma da makiyaya duba da yadda aka fuskaci damina wanda kuma alokaci daminane akafi samun rikici a tsakanin manoma da makiyaya. Don hakane ya kamata akirayi manoma da makiyayan da sukasance masu kai zuciya nesa a duk lokacinda wani abu ya shiga tsakaninsu. Alhaji Bello yace manoma da makiyaya su sanifa su yan uwan junane don haka bai kamata ace ana samu ta kaddama a tsakaninsuba. Saboda haka ya kamata sukasance masu doka da ka ididin noma da kiwo a koda yaushe. Bello ya kuma kara da cewa sun tattauna da kwamandan rundunan tsaro farin kaya wato civil defence na jahar Adamawa dangane da mataken da za a dauka domin dakile dukkanin matsaloli da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya a fadin jahar baki daya. Ya kuma kirayi gwamnatin da ta taimaka wajen shiga tsakani wajen samarwa makiyayan wadaceccen burtali wanda haka zai taimaka wajen kawo karshen rikici a tsakanin manoma da makiyaya.

Comments

Popular posts from this blog

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie

TSARO: AN BUKACI YAN NAJERIYA SUKASANCE MASU BAIWA HUKUMOMIN TSARO HADIN KAI DA GOYON BAYA.