Majalisar harkokin addinin Musulunci a karamar hukumar yola ta arewa takudiri aniyar koyarwa yaran sanin watannin addinin Musulunci.

majalisar harkokin addinin musulunci a karamar hukumar yola ta arewa ta sha alwashin ganin ta wayarwa dalube Kai dangane da sanin watannin addinin musulunci dama shekaran. Shugaban majalisar harkokin addinin musulunci a yola ta arewa Alhaji Abdullahi Abubakar Butu ne ya baiyana haka a lokacinda yake amsa tambatoyi daga manema a yola. Alhaji Abdullahi Butu yace yanzu haka suna Shirin rarrabawa makarantun Islaniyoyi takardu wadanda suke dauke da watannin addinin musulunci dama kalandar ta addinin musulunci. A cewarsa dai karantar da yara sanin watannin addinin tun suna matakin islamiya zai taimaka wajen wayarwa jamma a Kai dangane da watannin na addinin musulunci. Ya Kuma kirayi iyayen da Suma su bada tasu gudumawar wajen fahintar da yaran sanin watannin addinin musulunci tun suna yara domin samun cigaban addinin musulunci.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie