Rundunan yan sandan jahar Adamawa tace tana tsare da mutane sama da dari wadanda ake zairgi da wawushe kayakin abinci.

Runduan yan sandan jahar Adamawa tace ta kama mutane da dama wadanda ake zargi da hanun a cikin wawushe kayakin abincin gwamnati dana al umma. A wata sanarwa da kakakin runduna yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ya aikewa manema labarai a yola, na cewa rundunan ta samu nasaran kama mttane akalla dari da goma (110) wadanda ake zargi da faffasa runbuna Adana abincin gwamnati tare da kwashe kayakin. Da wannan ne rundunan ke gargadi al umma da su kaucewa dukkanin abinda zai haifar da matsaloli a tsakanin Al umma. A cewar kakakin rundunan yan sandan rundunan a shirye take ta saka kafar wando daya da duk wanda yayiwa doka karan tsaye.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie