Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya fara horar da mata yan Jarida na kwanaki uku a jahar Taraba.

Daga Ibrahim Abubakar Jalingo
Ofishin jakadancin Amurka dake Najeriya ya fara horar da mata yan Jarida na kwanaki uku a jahar Taraba domin inganta aiyukansu a zamunance ba tare da fargaba ba da Kuma bada rahoton da zai kawo cigaba a yankin arewa masau gabas.
Horan wanda ofishin jakadancin Amurka tare da hadin gwiwar kungiyar na Organization for Innovation anda Sustainable Development suka shirya a wani matakin na Samar da dai daito aikin Jarida ga mata a yakin na arewa masau gabashin Najeriya.
Yan Jarida mata a jahar Taraba dai na fuskantar kalubale da dama a duk lokacinda suke gudanar da aiyukansu a Arewacin Najeriya. Wani masana dai na cewa horon zai karwa matan kwarin gwiwar gudanar da aiyukansu bisa kwarewa domin ganin an samu nasaran cigaban dama wanzar da zaman lafiya a yankin na arewa masau gabas dama kasa baki Daya.
Sama da mata dari da hamsin ne dai ake saran zasu samu horon a yankin arewa masau gabas domin ganin mata su samu kwarewa wajen aikin Jarida. A cewa ofishin Jakadancin Amurka dake Najeriya.

Comments

Popular posts from this blog

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie

TSARO: AN BUKACI YAN NAJERIYA SUKASANCE MASU BAIWA HUKUMOMIN TSARO HADIN KAI DA GOYON BAYA.