Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya fara horar da mata yan Jarida na kwanaki uku a jahar Taraba.

Daga Ibrahim Abubakar Jalingo
Ofishin jakadancin Amurka dake Najeriya ya fara horar da mata yan Jarida na kwanaki uku a jahar Taraba domin inganta aiyukansu a zamunance ba tare da fargaba ba da Kuma bada rahoton da zai kawo cigaba a yankin arewa masau gabas.
Horan wanda ofishin jakadancin Amurka tare da hadin gwiwar kungiyar na Organization for Innovation anda Sustainable Development suka shirya a wani matakin na Samar da dai daito aikin Jarida ga mata a yakin na arewa masau gabashin Najeriya.
Yan Jarida mata a jahar Taraba dai na fuskantar kalubale da dama a duk lokacinda suke gudanar da aiyukansu a Arewacin Najeriya. Wani masana dai na cewa horon zai karwa matan kwarin gwiwar gudanar da aiyukansu bisa kwarewa domin ganin an samu nasaran cigaban dama wanzar da zaman lafiya a yankin na arewa masau gabas dama kasa baki Daya.
Sama da mata dari da hamsin ne dai ake saran zasu samu horon a yankin arewa masau gabas domin ganin mata su samu kwarewa wajen aikin Jarida. A cewa ofishin Jakadancin Amurka dake Najeriya.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.