Rundunan yan sanda a jahar Adamawa ta kama wani da ake zargi dayiwa yar shekaru fyade.

Rundunan yan sanda a jahar Adamawa tayi nasaran cafke wani da ake zargi da yiwa wata yarinya yar shekaru hudu da haifuwa fyade. Kakakin rundunan yan sandan a jahar Adamawa SP Suleiman Yahay Ngurojene ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwan tace mutumin da ake zargi mai shekaru talatin da biyu da haifuwa wato Mika Bitrus wanda yake zaune a Garin Sangere kan titin zuwa Girei wanda kuma ana zarginsa da yuwa wata yarinya mai shekaru hudu da haifuwa fyade. An dai samu nasaran damke mutuminne biyo bayan karafi da uwar yarinyar Fatsuma Abdullahi da shigar a ofishin yan sanda dake Girei, wanda kuma hakan yasa rundunan yan sandan batayi kasa agwiwaba wajen gudanar da bincike akan lamarin. Bincike da aka gudanar ya baiyana cewa shi wanda ake zargin dai masana ar kafintane kuma ya aikata laifinne ga yar makwabcinsa. Tunin dai kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya bada umurnin gudanar da bincike dangane da lamarin kuma da zaran an kammala bincike za a gurfanar da wanda ake zargin gaban kotu domin ya fuskaci shariya.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie