Tashin bom yayi sanadiyar kashe mutane 50 a Pakistan.

.
Akalla mutane hamsin suka mutu wasu hamsin kuma suka jikkata sakamokon harin kunan bakin wake da aka kai a wurin bikin Maulidi a Pakistan kamar yadda hukumar Yan sandan kasar ta baiyana. Lamarin dai ya farune a kusa da masallaci dake arewa masau yamma na lardin Balochistan a dai dai lokacinda ake gudanar da bikin Maulidi tunawa da ranan haifuwar mazon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. Yanzu haka dai hukumomi a lardin na Balochistan sun aiyana dokan ta baci domin maida da zaman lafiya a yankin. Kawo yanzu dai ba wata kungiya da ta dauki nauyin Kai harin. An sake samun tashin wani bom a masallaci dake kusa da birnin Peshawar a Khyber dake lardin Pakhtunkhwa. Sai dai har yazuwa yanzu ba Akai ga gano wadanda suka jikkata ko rasa ratukaba. Duk da cewa bom din yayi sanadiyar lalata gine ginen masallacin.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie