An buiaci mata su maida hankali wajen baiwa yara tarbiya..

An kirayi mata musulmai da sukasance masu Neman ilimin addinin musulunci da Kuma tura yaransu makarantu domin su samu ilimin addinin dana zamani Wanda acewarta hakan zai taimaka wajen samun yara na gari dama ingancaccen tarbiya a tsakanin yara. Amiran kungiyar mata musulmai ta tarayya wato FOMWAN Shiyar jahar Adamawa Khadija Buba ce tayi wannan kira a zantawarta da manema labarai Jin kadan da kammala taron Da awa da aka gudanar a Victim dake cikin karamar hukumar a jahar Adamawa. Malama Khadija tace Neman ilimi wajibine ne ga Al umma musulmai don haka Yana da muhimmanci Al umma musulmai su dukufa wajen Neman ilimi tare Kuma da tura yaransu makarantu domin su samu nagarceccen ilimi sukasancewa sune shuwagabanin gone. Ta Kuma shawarci shuwagabanin dama malamai da su tashi tsaye wajen fadakar da Al umma mahimmancin zaman lafiya da hadin Kai a tsakanin Al umma. Wanda acewarta hakan zai kawo cigaba dama zaman lafiya Mai daurewa. Harwa yau da kirayi Yan Najeriya da sucigaba da yiwa kasa adu o I domin Neman taimakon Allah Madaukakin sarki wajen kawo karshen dukkanin kalubalen tsaro a fadin Najeriya baki Daya.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie