An bukaci mabiya addinin kirista da suyi amfani da wannan lokaci wajen yin adu o I zaman lafiya..

Gidauniyar Attarahum a jahar Adamawa tana Mai taya mabiya addinin kirista bikin kirsimeti dafatan za ayi bikin lafiya. Shugaban Gidauniyar ta Attarahum na jahar Adamawa Mallam Mukhtar Dayyib ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Bayan taya murnan sanarwan ta Kuma kirayi mabiya addinin kirista da suyi amfani da wannan lokaci wajen yiwa jaha dama kasa adu o I Samar da zaman lafiya dama neman taimakon Allah Madaukakin sarki wajen kawo karshen dukkanin kalubalen tsaro a fadin Najeriya baki Daya. Sanarwan ta Kuma kirayi jama a da sukasance suna taimakawa hukumomin tsaro da wasu bayanai da zai taimaka wajen dakile aikata laifuka a tsakanin Al umma. Da wannan nema ake kira ga iyaye da su maida hankalin kan yaransu domin ganin ba a samu wata matsalaba a lokaci dama bayan bikin na kirsimeti.

Comments

Popular posts from this blog

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie

TSARO: AN BUKACI YAN NAJERIYA SUKASANCE MASU BAIWA HUKUMOMIN TSARO HADIN KAI DA GOYON BAYA.