Wata matashiya tayi Kunan bakin wake a jahar Adamawa.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta samu rahoton cewa wata matashiya yar shekaru 22 da haifuwa Mai Suna Florence Vandi ya hallaka kanta biyo bayan Shan maganin kashe kwari wato otafiyafiya. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola. Ita dai marigayiya Florence yar karamar hukumar Munchikace Kuna tana zaune a Viniklang dake cikin karamar hukumar Girei a jahar Adamawa.ta Kuma Yi sanadiyar hallaka kantane biyo bayan damuwa da tayi sakamokon mutuwar saurayinta. Kuma ta dauki mataki hakanne Sa o I kadan bayan rasuwar saurayin nata Mai Suna Nuhu Boniface Wanda ya mutu sakamokon gajeriwar rashin lafiya da yayi fama da ita. Bin cike ya nuna cewa kafin rasuwar Florence ma aikaciyace a hukumar kiwon lafiya a matakin farko dake karamar hukumar Girei. Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya baiyana damuwarsa dangane da aukuwar lamarin don haka nema ya shawarci Al umma da su daina daukan doka a hanunsu da zaran sunga abunda bai kamataba su Kai rahoto zuwa ofishin Yan sanda mafi kusa.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie