Kungiyar malamain Jami o I a Najeriya ASUU ya yabawa gwamnatin tarayya kan cire Jami o I daga tsarin biyan Albashi na IPPIS.

malamain Jami o I a Najeriya wato ASUU ta yabawa gwamnatin maici karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu bisa kokarinta na cire Jami o in Najeriya dama sauran manyan makarantu daga tsarin biyan albashi na IPPIS a wani mataki na inganta manyan makarantu dake fadin Najeriya Shugaban Kungiyar ta ASUU shiyar Jami ar Modibbo Adama dake Yola Dr El Maude Jibrin ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. A cewarsa cire Jami o in Najeriya dama wasu manyan makarantu daga tsarin na IPPIS da akayi a kwanan nan Yana Daya daga cikin matakai da wannan gwamnati karkashin shugaban Bola Ahmed Tinubu na inganta tsarin Jami o I dake fadin Najeriya. Dr El Maude yace gwamnatin da ta gabata karkashin tsohon shugaba Muhammadu Buhari ala tilas ta sanya Jami o I dama manyan makarantu cikin tsarin na IPPIS . Dr El Maude Jibrin ya Kuma yaba da kokarin da ministan ilimi Farfesa Tahir Mamman yakeyi na tabbatar da ganin an cire Jami o I dama sauran manyan makarantu daga tsarin na biyan albashi na IPPIS. Ya Kuma bukaci ministan da ya maida hankalin kan yarjejeniua da kungiyar ta ASUU ta cimma da gwamnati tun a shekara ta 2016 Wanda ya hada da alawus alawus nasu da dai sauransu. Ya Kara kira ga gwamnati da tayi dukkanin maiyiwa domin inganta yanayin aiyukan Jami o I domin cigaban kasa baki Daya.

Comments

Popular posts from this blog

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie

TSARO: AN BUKACI YAN NAJERIYA SUKASANCE MASU BAIWA HUKUMOMIN TSARO HADIN KAI DA GOYON BAYA.