Gwamnatin jahar Taraba Tasha alwashin inganta sashin kiwon lafiya a fadin jahar.

 



Daga Sani Yarima Jalingo


Gidauniyar Theophilus Yakubu Danjuma ya gyara asibitin zamani na ciwon ido dake cikin karamar hukumar Takum a jahar Taraba Wanda gwamnan Agbu Kefas ya Bude .





A yayin bikin budewar gwamna Kefas ya baiyana godiyarsa ga Gidauniyar na TY Danjuma bisa kokarin Gidauniyar na gudanar da aiyukan cigaban jahar.




Ya yaba da  gudumawar da sanata Daisy Danjuma bisa gyara asibitin jinya ido a cikin karamar hukumar Takum wannan abun cigabane.




Da yake magana a wurin bikin Danjuma yace an gudanar da wannan aiyuka ne da suke da muhimmanci domin kawo zaman lafiya da Kuma baiwa masu sha awar zuba jari da suzo su zuba jarinsu.





Ya Kuma baiyana cewa akwai bukatar inganta sashin sadarwar zamani tare da horarwa domin samun cigaban jahar.



Joshua Campenee. Shine darectan raya yankin Afirka ne a Najeriya yace asibitin zaitaimaka wajen inganta kiwon lafiya a fadin jahar.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.