Rundunan Yan jahar Adamawa ta maido da zaman lafiya a kauyuka da suke kananan hukumomin Numan da Demsa.

 



Biyo bayan Kai ruwa rana da aka samu a tsakanin Al ummar Selfi da Pkasham wadanda ke cikin kananan hukumomin Numan da Demsa a jahar Adamawa lamaeinda yayi sanadiyar mutuwar mutane uku 



Tunun dau kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Dankombo Morris ya tura jaimi an Yan sandan domin maido da zaman lafiya da Kuma doka da oda a yankunan.




Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.




Sanarwan tace a yanzu haka lamura sun koma daidai Kuma ana cigaba da bincike domin kama wadanda suke da hanu a cikin rikicin. 




Kwamishinan Yan sandan ya kirayi mazauna yankin da su rugumi zaman lafiya su kaucewa duk abinda zai haifar da matsala a tsakaninsu.saboda haka sugudanar da aiyukansu batare da fargaba ba su Kuma Kai rahoton duk

 Wanda ba su amince da lamarinsa zuwa ga ofishin Yan sanda mafi kusa.ko Kuma Akira wadananan lambar waya.08089671313.08034037570.


Kwamishinan yan sandan ya tabbatarwa gwamnati da ma Al mar jahar Adamawa cewa rundunan zata hukunta duk Wanda aka kama da aikata irin wadannan lafika domin rundunan bazata nade hanunta tana kallo ana tada hankaliba.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie