Yan Sanda a jahar Adamawa sun takawa Yan shila birki.

 


Daga Ibrahim Abubakar Yola.

A kokarin dakile aiyukan Yan shila ofishin Yan sanda dake Jimeta wato Jimeta Division dake cikin karamar hukumar yola ta arewa a jahar Adamawa ta Yi nasaran kama mutane goma sha biyar Yan shila a dai dai lokacinda suke yiwa mutane fashi da makami a runde.



Rundunan tare da hadin gwiwan Yan banga sun kama mutane 15 cikin gungun mutane dake aikata ba dai daiba.



Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa.



An dai kama mutanen ne tare da makamai masu hatsarin haske. Da suka hada da wukake, adduna da dai sauransu. Tare da wayoyin hanu biyu.


Sanarwan tace da zaran an kammala bincike za a gurfanar da su gaban kotu domin su fuskanci shariya.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie