An baiyana cewa hadin Kai Yana da muhimmanci i a tsakanin Al umma.

 


Daga Sani Yarima Jalingo.


Shugaban karamar hukumar Jalingo a jahar Taraba Dr Aminu Jauro Hassan yayi Kiran kan hadin Kai domin baiwa gwamna Agbu Kefas damar cika muradunsa na aiyukan cigaban jaha.



Shugaban yayi wannan kirane a lokacin da ake rantsar da mutane 7 masu sanya ido kan kansiloli, tare da masu bada shawaran 12 dama shugaban ma aikata Wanda aka gudanar a harabar karamar hukumar ta Jalingo.



Dr Aminu Jauro Wanda ma shine shugaban kungiyar shuwagabanin kananan hukumomi wato ALGON shiyar jahar Taraba  yace Yana da muhimmanci a maida hankali wajen yin dukkanin abinda zai kawo cigaban Al umma.



Dr Jauro ya shawarci sabbin wadanda aka rantsar din da su taka nasu rawan da zai kawo cigaba a dukkanin Al umomin yankin.



Ya Kuma yabawa gwamna Agbu Kefas bisa kokarinsa na gudanar da aiyukan cigaban jahar.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie