An baiyana cewa hadin Kai Yana da muhimmanci i a tsakanin Al umma.

 


Daga Sani Yarima Jalingo.


Shugaban karamar hukumar Jalingo a jahar Taraba Dr Aminu Jauro Hassan yayi Kiran kan hadin Kai domin baiwa gwamna Agbu Kefas damar cika muradunsa na aiyukan cigaban jaha.



Shugaban yayi wannan kirane a lokacin da ake rantsar da mutane 7 masu sanya ido kan kansiloli, tare da masu bada shawaran 12 dama shugaban ma aikata Wanda aka gudanar a harabar karamar hukumar ta Jalingo.



Dr Aminu Jauro Wanda ma shine shugaban kungiyar shuwagabanin kananan hukumomi wato ALGON shiyar jahar Taraba  yace Yana da muhimmanci a maida hankali wajen yin dukkanin abinda zai kawo cigaban Al umma.



Dr Jauro ya shawarci sabbin wadanda aka rantsar din da su taka nasu rawan da zai kawo cigaba a dukkanin Al umomin yankin.



Ya Kuma yabawa gwamna Agbu Kefas bisa kokarinsa na gudanar da aiyukan cigaban jahar.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.