Jam iyar APC ta lashe zaben shuwagabanin kananan hukumomi a fadin Jahar Gombe.

 




Jam iyar APC Mai Mulki a jahar Gombe ta lashe dukkanin kujerun shuwagabannin kananan hukumomi 11 dake fadin jahar harma da kansiloli 114 a jahar ta Gombe.



Da yake sanar da sakomokon zaben shuwagabanin kananan hukumomi da akayi a fadin jahar Saidu Shehu Awak yace kansiloli 114 sunyi nasaran cin zaben ne batare da abokan hamaiyaba, hakama jam iyar tayi nasaran cinye dukkanin shuwagabanin kananan mukumomi 11 dake fadin jahar.



A cewarsa a kalka jam iyu biyar ne suka shiga zaben da suka hada da PDP. ANPP. YPP. ZLP da Kuma jam iyar Accord.




Jami in tattara sakamokon zaben ya godewa jam iyu da suka shiga zaben dama Al umma jahar bisa yadda suka bada hadin Kai domin yadda aka gudanar da zaben lafiya.




Da yake magana a madadin jam iyu da suka shiga zaben shugaban  kungiyar dake shiga tsakanin jam iyu IPAC Kuma shine shugaban. Jam iyar Accord a jahar Gombe Alhaji Muhammad Adamu ya amice da Kaye da yasha tare da taya murna ga jam iyar APC bisa nasara da ta samu ya Kuma baiyana farin cikinsa dangane da yadda jam iyarsa tazo na biyu.



A ranan asabar da ta gabata ne dai aka gudanar da zaben shuwagabanin kananan hukumomi da kansiloli a fadin jahar ta Gombe.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie