Wanda ake zargi da satar mota ya shiga hanu a jahar Adamawa.

 



A yanzu haka rundunan yan sanda a jahar Adamawa tana tsare da wani mai suna Ibrahim Ali  da ake zarginsa da satar karamar mota Kiran sitalen  Mai dauke da nimbar rijista JMT 317 RA.



An samu nasaran kama Wanda ake zargin ne a shingen binciken ababen hawa dake Ngurore Kuma ya tabbatar da aikata lafin indama yace ya saci motar ce a wani wuri dake cikin garin Jimeta dake karamar hukumar yola ta Arewa fadar gwamnatin jahar Adamawa.



Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.



Sanarwa ta baiyana cewa kwamishinan yan sanda jahar Adamawa Dankombo Morris ya kirayi Al umma musammanma wadanda aka Wanda aka satar masa mota da yaje ofishin yan dake Nguroje da yayi bayani domin ya karbi kayansa.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.