An yabawa gwamnatin jahar Adamawa bisa aiyukan cigaban jahar

 



An yabawa gwamnatin jahar Adamawa karkashin jagorancin gwamna Ahmadu Umaru Fintiri bisa kokarinta na aiyukan cigaban jahar.


Shugaban kungiyar Sullubawa ta kasa shiyar jahar Adamawa Alhaji Bello Ardo ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa.


Alhaji Bello yace gwamnatin ta taka rawan gani a bangarori daban daban da suka hada da ilimi, kiwon lafiya, tsaro, tattalin Arziki, hanyoyi, da dai sauransu.

Don haka nema kungiyar Sullubawa ke taya Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri murnan cika shekara Daya akan Mulki a wa adi na biyu, Wanda ya gudanar da aiyukan cigaban Al ummar jahar ta Adamawa.


Alhaji Ardo ya shawarci daukin Al ummar jahar Adamawa da sukasance masu baiwa gwamnatin Ahmadu Umaru Finti hadin Kai da goyon baya, da Kuma Yi masa adu ar Allah ma daukakin Sarkin ya bashi damar cigaban da aiyukan cigaban jahar.


Ya Kuma tabbatar da cewa kungiyarsu a shirye take ta baiwa gwamna Ahmadu Umaru Finti goyon baya a Koda yaushe domin ganin ya samu nasaran gudanar da shugabancinsa yadda ya kamata ba tare da matsaloliba.


Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie