Rundunan yan sandan jahar Adamawa tana cin nasaran yaki da masu aikata laifuka a fadin jahar.

 



A kokarinta na yaki da masu aikata laifuka dama watsar dasu daga maboyarsu daban daban da suka hada da Jimeta bypass, Jambutu, Yokkore, Tashan Tiopa, da Kuma kwalbatin Doubeli. Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta kama mutane 39 da ake zargi da aikata laifuka Wanda kawo yanzu ana cigaba da bincike kuma za a tabbatar da adalci a yayin bincike.


Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.


Sanarwan ta Kuma shawarci daukacin Al ummar jahar Adamawa da sukasance masu taimakawa hukumomin tsaro da wasu bayanain duk abinda basu amince da suba domin daukan matakin da ya dace Akai.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie