Gidauniyar AYTAM: An rantsar fa kwamitocin. da zasu gudanar da musabakar karatun Al Qur ani ga marayun a jahar Adamawa.

 



A yayinda ya rage kwanaki kadan a gudanar da gasar Karatun Al Qur ani Mai girma ga marayu zalla, a jahar Adamawa. Hakimin Hong Umar Babangida Mahmud ya kaddamar da kwamiticin da zasu gudanar da musabakar a jahar ta Adamawa.



An gudanar da bikin kaddamar wanne a harabar karantar Al Huda dake Bachure dake nan Yola.



Da yake jawabi Hakimin Hong Kuma Danmaliki Adamawa Alhaji Umar Babangida Mahmud Wanda Kuma shine shugaban gidauniyar AYTAM  a jahar Adamawa yace AYTAM ta shiryawa marayu gasan ne domin Suma su samu damar shiga a dama dasu a cikin harkokin gasar Karatun Al Qur ani inda yace daga cikinsune za a zabi wadanda zasu wakilci jihar Adamawa a matakin kasa.



Hakimin na Hong ya Kara da cewa za a fara gasar ne daga ran Jumma a 26-7-2024 Wanda Kuma za a kammala a ranan lahadi 28-7-2024.




Da yake bada shawara Dr Aliyu Abdullahi Basullube ya kirayi iyaye da su maida hankali wajen karantar da yaransu ilimin addinin musulunci domin samun yara na gari a tsakanin Al umma.




Itama a jawabinta mataimakiyar amiran AYTAM ta kasa Hajiya Asmau Abubakar yace wannan gasar da za a gudanar shine karo na biyu a jahar Adamawa.




Tace wannan damace ga marayu da Suma zasu nuna nasu basira musammanma a bangaren karatun Al Qur ani Mai girma.




Kwamiticin da aka kaddamar dai sun hada dana Kudi, Saukar da baki, bada Kaututtuka, Abinci, Tsaro, Watsa labarai da dai sauransu.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie