Wasanni: An yabawa gwamnatin gwamna Agbu na jahar Taraba kan harkokin wasanni.

 




An yabawa gwamnatin gwamna Agbu Kefas na jahar Taraba bisa kokarinsa na bunkasa harkokin wasanni a fadin jahar.



Shugaban kwamitin harkokin wasanni  da matasa a majalisar dokokin jahar Taraba Kuma Dan majalisar Mai wakiltar Karim Lamido Ii a majalisar dokokin jahar Taraba Hon. Anas Shu aibu ne ya baiyana haka a zantawarsa da manema labarai a Jalingo.




Hon. Shu aibu  Wanda Dan Jam Iyar APGA ne ya yabawa gwamna kan ma mijin kokari da yake na inganta rayuwar matasa harma da bunkasa wasanni a fadin jahar.



Hon. Anas yace kasancewa gwamna Mai Sha a war wasanni ne don haka akwai bukatan maida hankali wajen bunkasa wasanni.




Hon . Shu aibu yace kasancewa wannan gwamnatin shekara Daya a kan Mulki Al umma jahar sn gani a kasa wajen bunkasa harkokin wasanni fiye da gwamnatoci da suka shude.





Yace ko a shiga gasar wasanni da jahar ta shiga a wasanni na ciki da wajen Najeriya da cigaba da wasan Olympic da ake Yi a jahar ya nuna cewa gwamna Kefas ya baiwa bangaren wasanni muhimmanci Wanda hakan zai taimaka wajen cigaban wasanni da matasa a fadin jaha.




Shu aibu ya Kuma yaba da nada Ambasado Joseph Joshua a matsayin kwamishinan wasani da matasa wannan ma cigaba ne a harkokin wasanni.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie