Shugaban kasa Bola Tinubu ya nada sabon shugaban hukumar Aikin hajji ta kasa. NAHCON.

 





Shugaban kasan Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da nada Farfesa Abdullahi Sale Usman a matsayin shugaban hukumar Aikin Hajji ta kasa wato NAHCON.



Mashawarci  na musamman kan harkan yada labarai ga shugaban kasa Ajuri Ngelale ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitara a litinin din nan.



Nada sabon shugaban na zuwa ne bayan sallama shugaban Hukumar ta NAHCON Malam Jalal Arabi Wanda shugaban kasar ya sallama biyona zarginsa da almudahana da kudin da yaki nera bilyon 90 Wanda gwamnatin tarayya ta baiwa hukumar a matsayin tallafi ga aikin hajjin shekara ta 2024.




An sallami Jalal daga kan mikamin shugabancin hukumar aikin hajji ta kasan ne bayan kwanaki hudu da hukumar dake yaki da cinhanci da rashawa wato EFCC  ta kamashi bisa tukumarsa da yin na daidaiba da kudaden hukumar.




Shugaban kasa yace Yana Mai tsammanin sabon shugaban zai gudanar da aiyukansu yadda ya kamata domin inganta hukumar.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie