Matsalar Wutan lantarki: Daluben kwalejin fasaha na jahar Adamawa sun gudanar da zanga zangan lumana.

 




Daga Ibrahim Abubakar Yola.


Da sanyar safiyar Litinin din nan ne dai daluben kwalejin fasaha ta jahar Adamawa suka gudanar da zanga zangan lumana  a wani abunda suka kira da rashin wutan lantarki a makarantar dama matsalar rashin ruwa Wanda acewarsa sun dauki dauki tsawon makwanni biyu batare da wutan lantarki ba.




Da yake yiwa manema labarai jawabi a madadin daluben Baba Lastiri ya baiyana damuwarsa dangane da rashin wutan dama ruwa tare da Kiran gwamnatin jahar Adamawa dama hukumar gudanarwan makarantar da su dauki matakan gaggawa domin magance matsalar baki Daya.



A cewarsa lamarin da yasa sai daluben sun fita wajen makarantar kafin debo ruwa saboda su sun gaji da haka saboda haka ne suke bukatar hukumomi suyi dukkanin Mai yiwa domin kawo karshen matsalar baki Daya.



Shima a jawabinsa shugaban kwalejin Farfesa Muhammed Tangos ya sanar da cewa kawo yanzu an shawo kan matsalar domin a cewarsa hukumar gudanarwan kwalejin suna iya kokarinsu domin ganin komai ya daidaita a kwalejin.




Shugaban kwalejin yace Yana Mai tabbatarwa Al umma cewa matsalar wutan Kam an shawo kan matsalar Kuma da yardan Allah komai zai koma daidai na tare da wata matsalaba.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie