Rundunan Yan sandan jahar Adamawa tana tsare da wani danbanga bisa zarginsa da yin sojan gona.

 





Rundunan yan sandan jahar Adamawa tayi nasaran cika hanu da wani danbanga da ake zargin da yin sojan gona inda yake ikirarin cewa shi Jami in dan sanda harma Yana damfaran mutane musammanma matuka keken Napep.




Wanda ake zargin Mai Suna Shafi u Abdulkadir Mai shekaru 27 mazaunin anguwar Yelwa ne dake cikin garin Jimeta a karamar hukumar yola ta arewa a jahar Adamawa.




Kakakin rundunan yan sandan dake jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa.




Sanarwan tace an samu nasaran kama Wanda ake zargin biyo bayan wasu bayanain sirri da da wasu Yan Sakai suka samu dangane da aiyukansu na cutar jama a inda aka sameshi sanye da kakin Yan sanda.




Sanarwan ta Kara da cewa da zaran an kammala bincike kan Wanda ake zargi za a gurfanar da shi a gaban kotu domin ya fuskanci shariya.




Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa Dankwambo Morris ya kirayi daukacin Al ummar jahar Adamawa da sukasance masu Kai rahoton duk wani batagari ga rundunan akan lokaci domin ganin an samu nasaran kare lafiyar Al umma.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie