Wasu da ake zargi da aikata laifuka sun shiga komar Yan sanda a jahar Adamawa.

 





A kokarinta na inganta tsaro da Kuma dakile aiyukan ta addanci a fadin jahar Adamawa rundunan Yan sandan jahar Adamawa yanzu haka tana tsare da wasu matasa hudu da ake zargin da addabar anguwar Jambutu dake cikin karamar hukumar yola ta arewa dake jahar Adamawa.



Anyi nasaran kama wadanda ake zargine a mahadar  Geriyo  da misalin karfe 2:00 am wato da dare Kuma an kama su da makamai masu hatsari da suka hada da wukake harma da tabar wiwi da dai dai sauransu.




Kakakin rundunan yan sanda jahar Adamawa SL Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola fadar gwamnatin jahar Adamawa.





Hakan na zuwane bayan koke koke da ake samu nayin fashi da makamai da sace sace da ake samu a cikin Al ummar yankin  Kuma a yanzu haka wadanda ake zargin suna hanun Yan sanda domin cigaba da bincike.





A sanarwan anjiyo kwamishinan Yan sanda jahar Adamawa Dankwambo Morris ya tabbatar da cewa rundunan a shirye take ta cigaba da kare rayuka dama dukiyoyin harma da inganta tsaro ga mazauna fadin jahar.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie