An bukaci gwamnatin jahar Adamawa da ta shiryawa matasa bita dangane da illar shaye shaye a tsakanin matasa.

 









An kirayi gwamnatin jahar Adamawa da tayi dukkanin abinda suka dace domin magance matsalar shaye shaye a tsakanin matasa a wani mataki na inganta rayuwar matasa a fadin jahar.





Shugaban kungiyar Izala na kasa Sheirk Abdullahi Bala Lau ne yayi wannan kira a lokacinda yake jawabi a wurin bikin yaye daluben mahaddata Al kur ani maigirma Wanda Makarantar NA IBI ta shirya a Yola.





Sheirk Abdullahi Bala Lau yace Yana da muhimmanci gwamnatin jahar Adamawa ta dauki matakin shiryawa matasa bita na musamman domin wayar musu da Kai dangane da illar ta ammala da muyagun kwayoyi tare da sauya musu tunani ta hanyar koyar dasu sana o I daban daban.




Sheirk Abdullahi Bala Lau ya baiyana cewa Jan matasan ajiki da Kuma wayar musu da Kai zaitaimaka wajen dakile matsalar shaye shayen a tsakanin matasa Wanda Kuma hakan zai basu damar inganta rayuwarsu yadda ya kamata.





Sheirk Abdullahi Bala Lau ya shawarci dukkanin masu ruwa da tsaki, sarakunan gargajiya, shuwagabanin addinai, shuwagabanin Al umma da suma su bada tasu gudumawa domin kawar da matsalar ta ammali da muyagun kwayoyi a tsakanin matasa dake fadin jahar.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie