Rundunan Yan sanda zata gudanar da Attisayen harbe harbe.







Rundunan Yan sandan jahar Adamawa tana Mai farin cikin sanar da jama a cewa zata gudanar da ATTISAYEN harbe harbe da Jami anta wadanda ke yaki da ta addanci wato CTU Wanda  za a gudanar akan titin zuwa Mubi dake cikin karamar hukumar Girei.





Kakakin rundunan Yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.




Ana saran gudanar da harbe harben za afara a ranan laraba 15-1-2025 Wanda zai dauki yini Daya.




Saboda haka ana shawartan dukkanin mazuna yankin, ko masu gudanar da kasuwanci, matukan ababen Hawa, manoma da makiyaya, da su kaucewa wurin da za a gudanar da harbe harben.




An sanar da Al umma cewa an dauki dukkanin  matakai tsaro  da suka dace domin bada kariya.




HAKAN NA KUNSHENE A CIKIN WATA SANARWA DA KAKAKIN RUNDUNAN YAN SANDAN JAHAR ASAMAWA SO SULEIMAN YAHAYA NGUROJE YA SANYAWA HANU A MADADIN KWAMISHINA YAN SANDA.

Comments

Popular posts from this blog

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie

TSARO: AN BUKACI YAN NAJERIYA SUKASANCE MASU BAIWA HUKUMOMIN TSARO HADIN KAI DA GOYON BAYA.