Rundunan Yan sanda zata gudanar da Attisayen harbe harbe.







Rundunan Yan sandan jahar Adamawa tana Mai farin cikin sanar da jama a cewa zata gudanar da ATTISAYEN harbe harbe da Jami anta wadanda ke yaki da ta addanci wato CTU Wanda  za a gudanar akan titin zuwa Mubi dake cikin karamar hukumar Girei.





Kakakin rundunan Yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.




Ana saran gudanar da harbe harben za afara a ranan laraba 15-1-2025 Wanda zai dauki yini Daya.




Saboda haka ana shawartan dukkanin mazuna yankin, ko masu gudanar da kasuwanci, matukan ababen Hawa, manoma da makiyaya, da su kaucewa wurin da za a gudanar da harbe harben.




An sanar da Al umma cewa an dauki dukkanin  matakai tsaro  da suka dace domin bada kariya.




HAKAN NA KUNSHENE A CIKIN WATA SANARWA DA KAKAKIN RUNDUNAN YAN SANDAN JAHAR ASAMAWA SO SULEIMAN YAHAYA NGUROJE YA SANYAWA HANU A MADADIN KWAMISHINA YAN SANDA.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie