Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta gano wasu shanu da ake zargin satosu akayi.









A kokarinta na yin sintiri domin kariya tare bankado aiyukan laifuka, Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta gano wasu shanu da aka sacesu.





Kakakin Rundunan Yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.



A yanzu haka Rundunan tana rike da shanun domin gudanar da bincike, Kuma da zaran an kammala bincike za a mikasu ga masu shi yadda ya kamata.




Kwamishinan Yan sandan jahar Adamawa *CP Dankwambo Morris psc(+),* ya kirayi Al umma musamman  wadanda shanunsu suka bata ko aka sace, da sukai rahoto a ofishin Yan sanda dake Numan da cikekken shaidar mallakar shanun domin karba.





Comments

Popular posts from this blog

Yola Zone: ASUU threatens to withdraw services on expiration of the 2-week ultimatum to FG

Breaking News: Muhammad Ahmad Song (Boboi/Baka)Passes Away at 83

ADAMAWA APEX CHOICE MOST INFLUENTIAL WOMEN IN ADAMAWA AWARD NIGHT