Antsinci Wani yaro Dan jahar Adamawa a jahar Kaduna.








MUHAMMAD ABUBAKAR Mai shekaru 8 da haifuwa,  a takaice dai an sanar da batansa tare da samunsa.





Kakakin Rundunan Yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Yola.



Yace shi Dan jahar Adamawa ne Wanda aka kaishi jahar Kaduna domin yin karatun addinin musulunci, Amma yanzu an sameshi a garin Kudaru dake karamar hukumar lere a jahar Kaduna.




Yaron yace iyayensa suna zaune a ta wajen filin wasa na wucin gadi, wato temporary stadium, dake cikin garin Jimeta cikin karamar hukumar Yola ta arewa, a jahar Adamawa.




Ana rokon duka Wanda Allah yasa ya san iyayensa ko yasan wadanda suke halaka da yaron ya tuntubi osfishin kakakin rundunan Yan sandan jahar Adamawa ko Kuma Alhaji Tukur Zubairu dake jahar Kaduna ta wadan Nan number wayoyi. 08136544154.

09015595292.





Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie