Gwamna Yusuf ya fitar da gargaɗi ga ma’aikatan gwamnati bayan murabus ɗin Namadi






Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya fitar da gargaɗi mai tsanani ga dukkan jami’an gwamnati bayan murabus ɗin Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi Dala, wanda ya yi murabus biyo bayan cece-kuce kan belin wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi.





A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne yayin taron majalisar zartarwa na 30 da aka gudanar a gidan gwamnati a ranar Laraba.


Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci duk wani hali da zai lalata ƙimar da ta gina ba, yana mai cewa duk jami’in da ya kasa riƙe amana ya fi dacewa da ya ajiye aikinsa.




Ya ce yaƙi da miyagun ƙwayoyi da sauran munanan dabi’u na daga cikin ginshiƙan gwamnatinsa, tare da gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu kai tsaye ko a kaikaice wajen irin waɗannan laifuka zai fuskanci hukunci.


Gwamnan ya kuma yi kira ga masu rike da mukamai su gudanar da ayyukansu bisa gaskiya, rikon amana da kima, domin kare mutuncin gwamnatin da suke wakilta.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie