An kaddamar da kwamitin neman Zaben Tinubu Ta Shatima a jahar Taraba.

An kaddamar da fara gangamin neman zabe shugaban kasa Bola Ahmed Tinibu da Shatima a karkashin jam iyar A P C a jahar Taraba. Ministan sifiri a Najeriya Alhaji Mu azu Sambo Jaji ne ya jagiranci kaddamar da kwamitin da zasuyi aikin nemana zaben Ahmed Bola Tinibu da Shatima a Jalingo fadar gwamnatin jahar Taraba. Da yake kaddamar da kwamintin Sambo ya kirayesu da suyi aiki tukuru domin hada kan yayan jam iyar ta A P C wanda hakan zai basu damar yin nasara a dukkanin matakai a fadin jahar baki daya. Ministan yace yana mai farin ciki da Allah ya nuna masa wannan rana na kaddamar da kwamitin da za su jagiranci gangamin neman zabe shugaban a jam iyar A P C wato Bola Tinibu da Shatima. Ya kuma baiyana cewa Jam iyar A P C jamiya ce da take da manufa mai kyau da kuma gudanar da aikin cigaban kasa. Don haka nema yake kira ga yan Najeriya da su baiwa jam iyar A P C kuria domin ta cigaba da gudanar da aiyukan cigaba da takeyi. Wasu daga cikin yayan jam iyar ta A P C sun baiyana farin cikin su dangane da wannan taro wanda acewarsu irin wannan taro zai taimaka wajen hadin kan yayan jam iyar ta A P C. Baya ga ministan wanda shine ko odinaton gangamin neman zaben Tinibu da Shatima a jahar Taraba a kwai yan majalisun dokokin jahar da sanatoci da dai sauransu a matsayin yan kwamitin.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie