Rundunan yan sandan jahar Adamawa tayi Babban kamu.

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta kama wasu mutane biyu wadanda suna ciki wadanda suka gudu daga gidan gyara halinka dake Kuje a Abuja. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar wanda kuma aka ranawa manema labarai a yola. Mutanen dai sune Atiku Ibrahim mai shakaru talatin da bakwai da haifuwa sai Adamu Ibrahim mai shekaru Arba in da haifuwa wadanda sun gudu daga gidan gyara halinkan ne biyo bayan hari da aka kai a gidan yarin na kuje a Raman 5-6-22. Wanda yayi sanadiyar mazauna gidan yarin akalla dari biyar suka gudu. Kuma ana tsare da sune bisa zarginsu da satan shanu dama sauran lafuka Wanda kuma suna zaune a gidan yarin ne tundaga shekara ta 2021.biyo bayan zarginsu da safaran makamai kuma su tabbatarwa rundunan jahar Adamawa cewa suna cikin wadanda suka gudu daga gidan yarin kuje. Kuma sun baiyana cewa sunama zaman jiran shariya ne a gidan yarin bisa zarginsu da safaran makamai. Kawo yan zu dai kwamishinan yan sandan jahar Adamawa Afolabi Babatola ya bada umurni da a gaggauta mikasu ga hukumar dake kula da gidajen gyara halinka dake jahar Adamawa domin daukan matakin da ya dace.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie