Sabon kwamandan Civil Defenve a jahar Adamawa ya fara aiki.

Sabon kwamandan Rundunan tsaron bada kariya ga farin kaya.wato Civil defence a Najeriya shiyar jahar Adamawa ya karbi ragamar mulkin rundunan a jahar Adamawa. Jami in watsa labarain rundunan a jahar Adamawa SC Dimas Yakubu Bille ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a yola wanda aka rabawa manema labarai. Sanarwan tayi nuna cewa kwamandan rundunan mai barin gado Muhammed Sanusi Bello ya mikawa Sabon kwamandan Ibrahim Mainasara ragamar mulkin rundunan a shelkwatar rundunan dake sakatariyar tarayya dake nan yola. Da yake jawabi kwamanda maibarin gado ya kirayi Jami an rundunan da sukasance masu baiwa Sabon kwamandan hadin kai da goyon baya a koda yaushe domin ganin an samu inganci tsaro a fadin jaha baki daya.ya kuma yabawa Jami an bisa jajircewarsu na ganin an samar da zaman lafiya a fadin jahar. Shima a jawabisa sabon kwamandan Ibrahim Mainasara yayi Alkawarin yin aiki kafada da kafada da Jami an rundunan domin samun cigaba da ma wanzar da zaman lafiya a tsakanin al umma dake fadin jahar. Ya kuma tabbatarwa gwamnatin jahar Adamawa dama al ummar jahar cewa rundunan a shirye take ta kare rayuka dama dukiyiyim Jama a. Don haka nema yake kira ga al ummar jahar da su kasance masu baiwa rundunan hadin kai da goyon baya domin ganin rundunan da samu nasaran dakile aiyukan ta addanci a fadin jahar ta Adamawa baki daya.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie