An baiyana irin muhimmanci da karatun Al qur ani mai girma yake dashi a tsakanin al ummah musulmai.

An kirayi Al ummah musulmai da su kara himma wajen gudanar da karatun All qur ani kai girma domin samun cigaban addinin musulunci yadda ya kamata a tsakanin Al ummah musulmai baki daya. Alhaji Sadiq Umar Daware ne yayi wannan kira a lokacinda yake jawabi a wurin bikin rufe gasar karatun Al qur ani mai girma wanda kungiyar gaskiya TV Africa shiyar jahar Adamawa ta shirya a yola. Alhaji Sadiq Daware wanda shine shugaban bikin yace karatun Al qur ani dama karantarwa yana da mutukan muhimmanci a tsakanin Al umma musulmai don haka akwai bukatan al umma musulmai sukasance masu runguman karatun Al qur ani domin samun daman yada addinin musulunci. Alhaji Daware ya kuma yabawa kungiyar ta Gaskiya TV bisa shirya wannan gasar karatun al qur ani mai girma ya kuma yi fatan zasu fadada aiyukansu har zuwa nahiyar Afirka baki daya. Ya kara kira ga al umma musulmai musammanma kungiyoyin addinin musulunci da suyi kasance masu shirya gasar karatun al qur ani mai girma domin samun cigaban addinin musulunci bak daya.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie