An shawarci yan agaji da sukasance masu taimakawa al ummah.

An shawarci yan agajin fityanul Islam da sukasance masu taimakawa al umma a bangarori daban daban musammanma a bangaren kiwon lafiya domin samun cigaban yadda ya Kamata. Darektan yan agajin fityanul Islam na jahar Adamawa Alhaji Sa idu Modibbo Buba ne ya bada wannan shawara a lokacinda yake jawabi a wurin rufe taron karawa juna sanin wanda aka shiryawa yan agajin anan yola. Alhaji Sa idu yace an shirya wannan taronne domin karawa yan agajin sanin makaman aiki da kuma yadda zasu maida hankali wajen taimakawa al umma a bangarori daban daban. Ya kuma kirayi yan agaji da sukasance masu nuna da a a duk lokacin da suke gudanar da aiyukansu domin samun cigaban kungiyar a tsakanin al umma baki daya. Alhaji Sa idu ya kirayi yan Najeriya da sucigaba da yin adu oi domin neman taimakon Allah madaukakin sarki wajen kawo karshen kalubalen tsaro a fadin Najeriya baki daya.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie