An yabawa gwamnnatin tarayya dangane da karantar da daluben firamare harshen uwa.

An yabawa gwamnatin tarayya bisa amincewa da a kararantar da daluben makarantin fimare da harshen uwa wanda hakan cigabane matuka. Alhaji Adamu Jingi yace gaskiya lamarin yayi dai dai wanda acewarsa ko kasashe da sukaci gaba a duniya suna karantar da dalubene da harshensu domon daluben su fahinci abinda ake koya musu yadda ya kamata. Don haka abinda gwamnatin tarayya tayi yayi dai dai kuma dafatan za a fadadashi zuwa makarantun gaba da firamare da kwalejoji harma da Jami o i domin hakane zai tai maka musammanma a bangaren likitoci, injiniyoyi, kimiya da fasaha da dai sauransu. Ya kuma kirayi masu ruwa da tsaki da sukasance masu bada hadin kai da goyon baya domin ganin gwamnatin ta cimma burinta na baiwa dalube inganceccen ilimi yadda ya kamata. Alhaji Jingi ya shawarci malamai makarantu musaman na firamare da su maida hankali sosai wajen karantar da dalube yadda ya kamata da kuma bin tsarin karantarwa wanda acewarsa hakan zai taimakawa daluben samun inganceccen karatu. Harwayau ya kirayi iyaye da su bada tasu gudumawa wajen karantar da yaran nasu ba tare da wata matsalaba domin acewarsa iyaye su suke da kaso mafi tsoka wajen baiwa yara tarbiya dama karatunsu.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie