Gidan Rediyo Najeriya fombina fm yola ya jajintawa Uba Dan Arewa.

Tawagan gidan Rediyon Najeriya Fombina FM yola sun kai ziyaran ta aziyar ga Uba Dan Arewa biyo bayan rasuwar mahaifins wato Alhaji Muhammed Dan malam Lau. Tawagan wanda Babban Manajan gidan Rediyo Najeriya fombina FM yola Alhaji Dahiru Garba Muhammed ya jagoranta. Inda yayi adu ar Alla madaukakin sarki ya jikansa ya kuma yi masa rahama yasa Aljannace makomansa. Yace a madadin gidan rediyo fombina yana mika ta aziyara ga iyalen marigayi inda ya baiyana rasuwar babban asarace baga iyalensa kawaiba harma da al ummah baki daya. Dayake jawabi a madadin iyalen marigayin wato Uba Dan Arewa ya nunu godiyarsa da jin dadinsa dangane da wannan ziyaran ta aziya wanda tawagan rediyo fombina suka kawo masa. Ya kuma yi adu ar Allah ma daukakin sarki ya bar zumunci tare dayin fatan Alheri ga ma aikata dama gidan resiyon baki daya. Alhaji Muhammed Dan Malam Lau dai ya rasune sakamokon gajeruwar rashin lafiya a cikin garin Lau dake jahar Taraba. Kuma ya rasu yana da shekaru casa in da biyu da haifuwa. Ya bar yara talatin da hudu tare da jikoki dari.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie