Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta kimtsa tsaf domin taran shugabann kasa Muhammadu Buhari.

A kokarinta na inganta tsaro da kuma dakile aiyukan ta addanci rundunan yan sandan jahar Adamawa tace ta kimtsa tsaf domin daukan dukkanin mataken da suka dace domin ziyaran da shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kawo jahar Adamawa. Kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a yola wanda aka rabawa manema labarai a yola. A sanarwan dai anjiyo kwamishinan yan sandan jahar Adamawa CP Sikiru Kayode Akande na cewa dukkanin shirye shirye ya kammala domin taran shugaban kasa do haka rundunan da sauran hukumomon tsaro sun hada kai domin ganin ba a samu matsalaba kafin dama bayan ziyaran shugaban kasa. Kwamishin yace za a takaita zirga zirgan ababen hawa a wuraren da shugaban kasa zaibi don haka al umma su kasance masu bin doka.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie