Gwamnatin jahar Adamawa ta bukaci da al ummar jahar su maida hankalin wajen yiwa jaha dama kasa adu o i.

Gwamnan jahar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya kirayi daukacin al ummar jahar Adamawa, tare da yan uwa da abokan arziki da su kaucewa taruwa da niyar yin bikin ranan haifuwarsa a ranan Jumma a 27-10-2023. Gwamnan Ahmadu Fintiri yace mai makon haka ya kamata ayiwa jahar Adamawa da kasa baki daya adu o I, ya kara da cewa Al umma suna bukatan tainakon gaggawa biyo bayan matsalar tattalin arziki da ake fama da shi sakamokon cire tallafin mai fetur da akayi. Babban sakataren watsa labarai gwamnan Humwashi Wonosiko ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a yola. Sanarwa tace mai girma gwamnan yace wannan yanayi da ake ciki na tsadar rayuwa wanda jama a ke fuskata wanda kuma hakan ya shafi tattalin arziki dama tsare tsaren gwamnatin tarayya. Domin magance matsalar a kwai bukatan a hada kai da kuma yin aiki tare domin samar da zaman lafiya da cigaban jaha dama kasa baki daya. A cewar gwamna Fintiri ba maganan bikin ranan haifuwa ne a gabanshiba, Al ummar jahar Adamawa ne a gabanshi saboda haka zaiyi dukkanin abunda suka dace domin ganin Al ummar jahar sun zauna cikin walwala. Harwayau gwamnan ya bada umurni yin adu o i a masallatai a ranan Jumma a da kuma a mujami u a rana lahadi domin neman taimakon Allah madaukakin sarki wajen kawo karshen kalubalen da aka fuskata sakamokon cire tallafin maifetur.

Comments

Popular posts from this blog

𝐀𝐃𝐀𝐌𝐀𝐖𝐀 𝐏𝐎𝐋𝐈𝐂𝐄 𝐂𝐎𝐍𝐅𝐈𝐑𝐌 𝐅𝐀𝐓𝐀𝐋 MOTOR 𝐀𝐂𝐂𝐈𝐃𝐄𝐍𝐓 𝐈𝐍𝐕𝐎𝐋𝐕𝐈𝐍𝐆 𝐌𝐈𝐋𝐈𝐓𝐀𝐑𝐘 𝐕𝐄𝐇𝐈𝐂𝐋𝐄 𝐀𝐍𝐃 𝐂𝐎𝐌𝐌𝐄𝐑𝐂𝐈𝐀𝐋 𝐁𝐔𝐒

ASUU MODIBBO ADAMA UNIVERSITY BRANCH COMMENCED TWO WEEK WARNING STRIKE.

NSCDC Adamawa State Command Deploys 2,521 Personnel for Easter Festivitie