Sakataren harkokin wajen Amurka ya gana da firaministan kasar Isra ila.

Karo na biyu a litinin din nan ne sakataren harkokik wajen Amurka Antony Blinken ya gana da firaministan kasar Isra ila a garin Tel Aviv. Tun a makon da ta gabatane dai sakateren harkokin kasar wajen Amurka ya gana da firaministan kasar ta Isra ila Benjamin Netanyahu bayan da Hamas ta kaddamar da hare hare masu karfi akan kasar ta Isra ila. Antony Blinnken ya tabbatar da cewa kasar Amurka zata baiwa kasar ta Isra ila goyon baya domin kasar ta kare kanta daga duk wani hari da za a iya kawo mata. Sama da Isra ilawa 1,400 ne dai suka hallaka a kwanaki tara da suka gabata biyo bayan da kungiyar Hamas ta kutsa cikin kasar ta Isra ila ta Gaza tare da kai hare hare lamarin da yayi sanadiyar mutuwar sojoji da fararen hula.

Comments

Popular posts from this blog

Rundunan yan sandan jahar Adamawa ta taimakawa iyalain Jamin an yan sanda da suka gamu da ajalinsu a bakin aiki.

Police in Adamawa Arrestet 31 year for serial theft.

Jambutu got new Chairman of PCRC.