Posts

Showing posts from February, 2023

Majalisar Addinin Musulunci a jahar Adamawa ta amice da Atiku Abubakar a matsayin dan takaran da zata zaba a matsayin shugaban kasa a zabe mai zuwa.

Image
Majalisar addinin musulunci a jahar Adamawa ta amice da dan takaran shugaban kasa a jam iyar P D P Alhaji Atiku Abubakar a matsayin wanda zasu zaba a matsayin shugaban kasa a zabe mai zuwa. Shugaban majalisar addinin musulunci dake jahar Adamawa Aljahi Gombo Jika ne ya baiyana haka a lokacin da yake yiwa manema labarai karin haske jin kadan da kammala taron majalisar wanda aka gudanar a sakatariyar majalisar dake yola. Alhaji Gambo Jika yace majalisar tayi la akari da yanayin yan takaran inda suka cimma matsaya ganin cewa Alhaji Atiku zasu baiwa kuri arsu domin kasancewarsa dan jahar Adamawa ne wanda kuma suna da yakiinin cewa zai gudanar da aiyukan cigaban kasan nan. Alhaji Jika yace majalisar ta kuma yabawa hukumomin tsaro bisa na mijin kokari da sukeyi wajen daukan dukkanin matakai da sukeyi domin kare rayuka dama dukiyoyin Jama a. Ya kuma jinjinawa gwamnan jahar Adamawa bisa kokari da yakeyi na gudanar da aiyukan cigaban jahar dama inganta t

An bukaci Babban Bankin Najeriya ya wadatar da sabbin kudade.

Image
Masu sana ar fawa a jahar Adamawa sun koka dangane da karancin kudi da ake fuskanta biyo bayan canja fasalin kudin Najeriya wanda haka yayi sanadiyar koma bayan harkokin kasuwancinsu na fawa. Alhaji Babanna Palace ne yayi wannan kira a tattaunawarsa da jardar Al Nur a yola. Dangane da karancin kudi da ake samu. Babanna yace ya kamata gwamnatin ta duba yanayinda al umma ke ciki na matsalar rayuwa domin ta dauki matakin magance matsalar. Wanda acewarsa mutane sun shiga wani yanayi na matsin rayuwa. Babanna yace Babban matsalarma itace wasu masu shanun basu da asusun ajiya a banki bale a tura musu kudi don haka ne ya zama wajibi su kirayi gwamnati da ta dubi lamarin domin samawa al umma saukin rayuwa. Da wannan ne yake kira ga Babban Bankin Najeriya da ya wadata bankuna da sabbin kudaden domin ganin al umma sun samu saukin gudanar da harkokinsu yadda ya kamata ba tare da matsalaba. Ya kuma kirayi yan Najeriya da sukasance masu gudanar da a

Rundunan yan sandan jahar ta Adamawa ta mika ta ziyarta ga iyalen marigayiya Maryam Abdullahi.

Image
Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa CP Afolabi Babatola a madadin rundunan yan sandan jahar Adamawa yana mai jajantawa iyalen marigaiya Maryam Abdullahi wanda ta gamu da ajalinta biyo bayan wani hatsaniya da ya faru a daren Alamis a kwalbatin Doubeli dake cikin karamar hukumar yola ta arewa. Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa wanda kakakin rundunan yan sandan jahar Adamawa SP Suleiman Yahaya Nguroje ya sanyawa hanu kuma aka rabawa manema labarai a yola. Kwamishina yan sandan ya nuna rashin jindadinsa da aukuwar lamarin kuma yace rundunan tana da kyakkawar halaka da al ummar jahar Adamawa don haka nema rundunan ta gaggauta mika ta aziuarta ga iyale dama yan uwa marigayiyar tare da yi mata adu ar Allah ya jikanta da rahama. Harwayau kwamishinan ya umurci mataimakin kwamishina mai kula da sashin binciken manyan laifuka wato CID da ya gaggauta bincike dangane da lamarin. Bayan mutawar Maryam Abdullahi yan zu haka rundunan tana tsare da Aliyu Yusuf.

An baiyana cewa rikicin jam iyar A P C a jahar Taraba bazai hanata nasaraba a zabe maizuwa.Hassan Ardo.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. Ko odinatan majalisar gangamin neman zaben dan takaran shugaban kasa a karkashi Jam iyar A P C Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima a jahar Taraba Ambasada Hassan Jika Ardo yace duk da rkicin cikin gida da ya dabaibaye jam iua A P C a jahar Taraba Jam iyar zatayi nasara a Babban Zaben ahekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Ambasada Hassan Jika Ardo ya bayyana haka ne a lokacinda ya zantawa da manema labarai a Jalingo fadar gwamnatin jahar Taraba. Tsohon Jakadan yace kan yayan jam iyar a hade yake don haka nema yake tabbatar da cewa jam iyar zatayi nasara a zabe mai zuwa. Ardo yace wasu makiyar jam iyar ne kawai ke kawo rudani a cikin jam iyar domin rarraba kan jam iyar wanda kuma baza su samu nasaraba domin kan jam iyar a jahar Taraba a hade yake asalima yan takaransu na jam iyar A P C zata samu naara a zaben majalisar dokoki ta kasa dana shugaban kasa wanda za ayi nan da makwanni. Domin a cewarsa a

An kirayi Babban Bankin Najeriya da ya wadatar da sabbin kudadea bankunan kasuwanci.

Image
An kirayai gwamnatin tarayya dama Babban Bankin Najeriya ta suyi dukkanin abunda suka dace domon wadatar da sbbin kudade a bankunan kasuwanci domin al umma su samu walwala biyo bayan kuncin rayuwa da suka shiga bayan canja fasalin kudaden Najeriya. Shugaban kunguyar masu sana ar P O S a jahar Adamawa Auwal Usman ne yayi wannan kira a zantawarsa da jarida Al Nur a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Auwal yace karancin kudi a bankunan kasuwanci dama hanun jama a yayi sanadiya tabarbarewar lamura da dama ya kuma sanya mutane ciki wahalar rayuwa, saboda haka ya kamata Babban Bankin na Najeriya da gwamnatin tarayya su taimaka a samar da wadattun kudade domin ceto mutane daga halin da suke ciki a yanzu. Ya kuma shawarci masu manyan shaguna da masu gidajen mai da su mallaki na uran P O S domin shima zai taimaka wajen samun saukin matsalar. Ya kuma yi fatan ganin an kammala Babban zaben shekara ta dubu biyu da ashirin da uku lafiya ba tare da wata m

An yabawa Al ummar jahar Adamawa bisa goyon baya da suka baiwa Hajiya Aishatu Binani.

Image
An yabawa al ummar jahar Adamawa bisa hadin kai da goyon baya da suka baiwa yar takarar gwamna a Jam iyar A P C Sanata Aishatu Dahiru Ahmed Binani a lokacinda ta gudanar da gangamin neman zabe a fadin jahar baki daya. Mallam Salihu Baba Ahmed ko odinatan gangamin yakin neman zaben sanata Aishatu Binani ne yayi wannan yabo a zantawarsa da jaridar Al Nur a yola radar gwamnatin jahar Adamawa. Mallam Salihu Ahmed yace Al ummar jahar Adamawa sunyi abun a yaba saboda yadda suka fito kwansu da kwarkwatarsu suka nunawa Hajiya Aishatu Binani goyon baya don akwai fatan ganin zasu bata kuri a a ranan zabe. Alhaji Salihu ya kuma jinjinawa matasa a fadin jahar Adamawa ganin yadda aka gudanar da dukkanin yakin neman zabe ba tare da yin amfani da makamiba kuma basu nuna halayen na ta ammali da miyagun kwayoyiba saboda haka yana gode musu kuma dafatan zasuci gaba da nuna halaye na gari a koda yaushe domin samun cigaban domokiradiya a jahar dama kasa baki daya.

Akalla malamai makarantun sakandare talatin ne suka samu horon kan wasanni a jahar Taraba.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. A kokarin ganin an samu cigaban kwallon raga a Najeriya wata kungiya mai zaman kanta wato kungiyar raya wasanin da ilimin Al umma CSED ta shiya horo kan wasan raga na kwanaki biyu wa malamain makarantun sakandare a jahar Taraba. Horon ya gudanane tare da hadin gwiwar cibiyar ta CSED da majalisar wasanin jahar Taraba Wanda ya gudana a dandalin wasa na Jolly Nyame wanda kuma ya samu halartar sama da malamai talatin. Da yake jawabi a wurin bikin rufe horon ko odinatan CSED ta kasa Edema Fuludu ya baiyana jin dadinsa dangane da wannan horon da akayiwa malamai wanda acewarsa hakan zai taimaka ba ga jahar kadaiba harma da kasa baki daya. Edema Fuludu wanda tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafar na Super Eagles ne ya kirayi gwamnatoci a dukkanin matakai harma da kungiyar kwallon raga a Najeriya ta su yi dukkanin maiyiwa domin ganin an samu cigaban kwallon raga a nahiyar Afrika baki daya. Yace an gudanar da horon ne

An samu gawar wani yaro da aka cire sassan jikinsa.

Image
A safiyar lahdin nan ne aka wayi gari da ganin gawar wani yaro karami mai kimani shekaru sha biyu, wanda aka cirewa maqoshi da idanu da kuma harshe, sannan aka jefar dashi a wani lungu a unguwar Rumde dake bayan sakatariyar karamar hukumar Yola ta Arewa a Jihar Adamawa. Ana kyauta ta zaton Yaron Almajiri ne da har zuwa lokacin hada wannan Rahoton ba'a kai ga gano a wace makaranta yake karatu ba. Sai dai duk kokarin da akayi domin jin ta bakin mazauna unguwar da lamarin ya faru, Mutanen duk sunki cewa uffan kan lamarin Wani jami'in tsaro daga Jimeta Division ya tabbatar da cewa sun dauki gawar zuwa mutuware dake asibitin kwararru na specialist dake jimeta.

An shawarci matasa wajen zabe shugaba.

Image
An kirayi matasa a fadin Najeriya da sukasance masu maida hankali wajen zaban shugaban da zai cire musu kitse a wuta ta wajen sama musu aikinyi domin dogaro da Kansu. Shugaban shuwagabanin matasan jam iyar P D P jahar Adamawa Hon. Abdulrahman Musa ne ya yi wannan kira a zantawarsa da jaridar Al Nur a yola. Hon. Abdulrahman yace matasa sune suke da kaso mafi yawa na Al ummar Najeriya da ma kada kuri a saboda da haka bai kamata ace sunyi wasa da wannan dama da suke dashi wajen yin bangan siyasaba ya kamata sukasane jakadu na gari a tsakanin Al ummah. Musa ya kuma kirayi yan Najeriya Musammanma yan siyasa da cewa siyasafa abunda zai rarraba kai bane asalima siyasa yana kawo hadin kai dama cigaba harma da wanzar da zaman lafiya. Ya kara da cewa yakamata yan Najeriya su zabi jam iyar P D P a dukkanin matakai domin ceto kasan daga hali da take ciki a yanzu. A cewarsa dan takaran shugaban kasa a jam iyar P D P Alhaji Atiku Abubakar jajirceccenen a bangaren