Posts

Showing posts from March, 2023

Za Kuga Chanji Cikin Kwanaki Dari na farko A Ofis- Zababben Gwamnan Taraba, Agbu

Image
Daga Sani yarima Jalingo. Za Kuga Chanji Cikin Kwanaki Dari na farko A Ofis- Zababben Gwamnan Taraba, Agbu Zababben Gwamnan Jihar Taraba, Kanal Kefas Agbu (mai ritaya) yace da yardan Allah zasu kawo chanji na zahiri cikin kwanaki dari na farko da za suyi a ofis. Agbu ya sanar da hakan ne a lokacin da yake yiwa dunbin magoya bayan Jam'iyyar su ta PDP yawabin godiya jim kadan bayan ya karfi takardan shedan zaben sa daga ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC dake Jalingo. Kwamishinan zabe na hukumar zaben mai zaman kanta ta INEC dake Jihar Taraba, Umar Muktar Gajiram shine ya mikawa zababben Gwamnan Jihar, Kanal Kefas Agbu (mai ritaya) takardan shedan zaben sa a ranar laraba 29 ga watan maris na 2023 da muke ciki. Hakanan kuma, Umar Muktar Gajiram ya mikawa suma zababbun 'Yan Majalisan dokokin jihar ta Taraba guda 24 takardan shedan zaben su a dakin da aka gudanar da tattara sakamakon zaben Gwamnan Jihar wanda ya gudana a ranar 18 ga watan maris din dake cikin h

An yaba da irin aiyuka gwamnat Ahmadu Umaru Fintiri yakeyi a jahar Adamawa.

Image
An yabawa. gwamnatin Ahmadu Umaru Fintiri bisa kakari da yayi wajen gudanar da aiyukan cigaban jahar Adamawa. Alhaji Abba Jambutu ne yayi wannan yabo a lakacinda ya tattauna da jarida All Nur a yola radar gwamnatin jahar Adamawa. Alhaji Abba Jambutu yace duba da irin kyawawan aiyuka da gwama Fintiri yayi ya kamata Al ummar jahar Adamawa su sake bashi damar cigaban aiyukan cigaban jahar harma da bunkasa tattalin arzikin jahar baki daya. Abba yace yakamata iyaye subaiwa gwamna damar cigaban da jagorantar gwamnatin duba da yadda ya maida hankali wajen bada ilimi kauta a fadin jahar ta Adamawa baki daya. Da wannan ne Alhaji Abba Jambutu ya kirayi daukacin Al ummar jahar Adamawa dda su fito kwansu da kwarkwatarsu da su zabi gwamna Fintiri domin ya sami damar cigaba da aiyukan cigaba da suka hada da hanyoyi, asibitoci, bada ilimi kauta, samarwa matasa aikinyi ta koya misu kananan sano o i har matama sun amfana da koyon sana o i karkashin gwamnatin

A zabi Binani wakili Boya.

Image
Zababben dan majalisar wakilain tarayyar Najeriya a mazabar Fufore Song Alhaji Aliyu Wakili Boya kuma sarkin matasan Adamawa yana mai kiran daukacin Al ummar jahar Adamawa da su fito ranan zabe su zabi Hajiya Aishatu Dahiru Binani a matsayin gwamna karkashin Jam iya A P C domin bata damar gudanar da aiyukan cigaban jahar baki daya. Wakili Boya yace yana mai kiran Jama a da su fito kànsu da kwarkwatarsu domin zaban Binani wanda tana iya kakarinta wajen samarwa matasa da mata aikinyi harma da koyardasu sanan o i daban daban. Saboda haka idan aka zabeta a matsayin gwamna zata samu damar bunkasa harkokin kasuwanci Wanda hakan zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin jahar baki daya.

Ban janyewa kowaba. Muhammed Shuwa.

Image
Dan takaran gwamna a jam iyar A D C a jajar Adamawa Alhaji Muhammed Shuwa yace shikam yana nan daram a matsayinsa na dan takaran gwamna a karkashin jam iyar A D C. Alhaji Muhammed Sshuwa yace baijanyewa kowaba asalima yana kira ga yan jahar Adamawa su fito kwansu da kwarkwatarsu a ranan zabe wato 18 - 3- 2023 domin su jefa mass kuri a. Ya kuma kirayi Al ummar jahar Adamawa da suyi watsi da jita jitan da ake yadawa na cewa ya jenye ya marawa wani dan takaran baya yace wannan batu ba haka yakeba. Shikam yana nan a maysayinsa na dan takaran gwamna a jam iyar A D C. Dan takaran gwamnan ya baiyanna haka ne a wata sanarwa da ya fitar a yola radar gwamnatin jahar Adamawa.

Wakili Boyi ya godewa mazabarsa bisa zabansa da sukayi.

Image
Alhaji Aliyu wakili Boya sarkin matasan Adamawa kuma wanda yayi nasaran cin zaben dan majalisar wakilain tarayyar Najeriya na mazabar Fufore da Song a jahar Adamawa, yana mai mika godiyarsa ga daukacin Al ummar jahar Adamawa musammanma mazabarsa bisa zabarsa da sukayi na dan majalisar wakilai tarayya, Alh. Wakili Boya yana mai farin ckin bashi dama da mazabarsa sukayi kuma da yardan Allah bazai basu kunyaba domin acewarsa zai dukkanin iya kakarinsa na kawo aiyukan cigaban mazabarsa. Don haka nema yake kara kira ga al ummar mazabarsa da sukasance masu yin adu o i wanzar da zaman lafiya a yankin da jaha dama kasa baki daya. Ya kuma bukacin al ummar su bashi hadin kai da goyon baya domin ganin ya samu nasaran gudanar da aiyukan mazabarsa cikin kwanciyar hankali ba tare da samun matsaloliba. Ya kuma shawarci matasa da sukasance masu bada tasu gudumawa wajen cigaban jahar dama kasa baki daya.

An bukaci da al umma musulami su maiada hankali wajen tura yaransu makarantun addini dana zamani.

Image
An kirayi iyaye da sukasance masu tura yaransu makarantu addinin musulunci domin ganin sun samu damar karatun All Qur ani mai girma domin ganin an samu wadattun makaranta Al Qur ani a tsakanin Al umma misulmai. Malam Aisha Adamu ce tayi wannan kira a lokacinda take yaye dalubenta wadanda suka sauke Al Qur ani mai girma a makarantarta da yola ta arewa fadar gwamnatin jahar Adamawa. Malama Aisha tace karantar da yara karatun Al Qur ani mai girma tun suna yara yana da mutukan muhimmanci wanda acewarta hakan zai taimaka wajen samun matass mahaddata Al Qur ani da dama a tsakanin Al umma musulmai wanda hakan zai kawo cigaban addinin musulunci. Ta kuma kirayi matasa da suma su maida hankali wajen neman ilimin karatun Al Qur ani mai girma domin suma su bada tasu gudumawa wajen cigaban addinin musulunci yadda ya kamata. Harwayau ta kirayi wadanda suka sauke da suyi amfani da karatun nasu domin ciyar da addinin musulunci gaba da kuma wanzar da zaman lafi

Dan takaran sanata. a jam iyar P R P a zabar kudancin jahar Taraba yaki amincewa da sakamokokn zaben sanata a na mazabar.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. Dan takaran sanata na mazabar kudancin jahar Taraba dan Jam iyar P R P Iliyasu Gadu yaki amincewa da sakamokon zaben majalisar dattawa da aka gudanar ranan 25-2-2023. Biyo bayan kin sanya tabbarin jam iyar ta P R P a takardan zabe tare da kiran hukumar zabe ta kasa INEC da tayi watsi da sakamokon zaben. Gadu ya baiyana hakane a taron manema labarai da ya gudanar a Jalingo fadar gwamatin jahar Taraba inda yaki amincewa da sakamokon zaben wanda ya baiwa dan takaran sanata na jam iyar A P C nasara. Yace hukumar zabe taki bin umurnin babbar kotun tarayya na umurni da aka bata da ta sanya tabbarin jam iyar a takardan zabe. A cewarsa yana daya daga cikin dubbain masu kada kuru a don haka ya fito yayi zabe kamar yadda doka ya tanada Amman abin takaicin shine baiga alamar jam iyarsuba a cikin takardan zaben sanata. Wannan ya nuna karara Nagoya bayansa basu samu damar zabansaba . Iliyasu yace baiga dalin da ya

Sanatan mazabar Arewacin jahar Taraba ya sake lashe zabe karo na biyu.

Image
Daga Sani Yarima Jalingo. Sanata mai wakiltan Mazabar Taraba ta arewa a majalisar dattawar Najeriya Sanata Shu aibu Isa Lau ya sake lashe kujeran sanata a yankin karo na biyu. Sanata Isa Lau wanda a yanzu haka shine mataimakin shugaban marassa rinjaye a majalisar dattawan Najeriya. Wanda kuma yayi nasara a zaben da aka gudanar a ranan asabar din da ta gabata. Yankin mazabar arewacin jahar Taraba dai sun hada kananan hukumomin Jalingo, Lau, Karim Lamido, Zing, Yaro, da kuma Ardo Kola. Da yake aiyana sakamokon zaben wanda ya baiwa sanata nasara mataimakin shugaban Jami ar tarayya dake Wukari Farfesa Chibiya Paul Chingu yace sanatan ya samu nasarane da kuri u dubu saba in da hudu da Dari shida da arba in da biyar inda abokin hamaiyyarsa Sani Abubakar Danladi yazo na biyu da kuri u dubu sittin da daya da dari takwas da saba in da takwas. Sanata Sani Abubak ar Danladi ya dai tsaya takaran sanata ne a karkashin jam iyar A P C

Anja hankalin matasa da suyi dukkanin abunda zai kawo cigaban kasa.

Image
An shawarci matasa dake fadin jahar Adamawa da su kasance masu hada Kansu da kuma yin dukkanin abinda suka dace domin samun cigaban rayuwarsu su kuma kasance masu shiga adama dasu a cikin harkokin siyasa domin suma su bada tasu gudumawa wajen cigaban jahar dama kasa baki daya. Sarkin matasan Adamawa kuma wanda yayi nasaran lashe zaben kujeran majalisar wakilain tarayyar Najeriya a mazabar Kananan hukumomin Fufore da Song a jahar Adamawa Alhaji Aliyu Wakili Boya ne ya bada wannan shawara a lokacin da ya marabcin tawagan matasa da suka kai mass ziyaran murnan nasara da yayi a zaben da aka gudanar a asabar din da ta gabata. Alhaji Aliyu Wakili yace matasa sune shuwagabanin gobe saboda haka ya kamata sukasance masu yin karatun ta nisu da kuma hangen nesa wanda acewarsa hakan zai taimaka wajen gudanar da aiyukansu yadda ya kamata. Wakili Boya wanda yayi samun nasaran lashe zabe a karkashin jam iyar A P C ya nuna godiyarsa ga daukacin Al ummar jahar Adamawa mus