Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta fara tantance masu aniyar shiga Yan sanda.
Daga Alhassan Haladu Yola.
Rundunan Yan sandan jahar Adamawa ta fara tantance masu aniyar shiga aikin Yan sandan wadanda ake kokarin diba a kwanan Nan, an fara gudanar da tantancewar ne a makarantar yaran Yan sanda dake barikin Yan sanda a karewa dake cikin garin Jimeta.
Hakan na kunshene a cikin wata sanarwa da kakakin Rundunan Yan sanda jahar SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya wallafa a ahafinsa na sada zumunta.
Sanarwan ta baiyana cewa shugaban sashin diban Yan sandan DCP Musa Bulus tare da shugaban tawagan Hukumar kula da harkokin Yan sanda Alhaji Bappai Abdullahi Suleiman da suke yiwa jami an da zasu gudanar da tantancewar jawabi sun kirayesu da su gudanar da aiyukansu bilhakki da gaskiya domin ganin an tantancesu cikin tsanaki ba tare da wata matsalaba.
Sanarwan tana mai sanar da wadanda ke Neman aikin Yan sanda da cewa ana gudanar da tantancewar ne kyauta tare da gargadin kaucewa duk abinda zai Karya doka domin tantancea ya gudana cikin lumana.

Comments
Post a Comment